< Firistoci 16 >
1 Ubangiji ya yi magana da Musa bayan mutuwar’ya’yan Haruna biyu maza waɗanda suka mutu sa’ad da suka kusaci Ubangiji.
After the two sons of Aaron died because they burned incense to Yahweh [in a manner that was contrary to what Yahweh commanded], Yahweh spoke to Moses/me.
2 Ubangiji ya ce wa Musa, “Faɗa wa ɗan’uwanka Haruna, kada yă riƙa shiga Wuri Mafi Tsarki bayan labule koyaushe, wato, a gaban murfi wanda yake bisa akwatin alkawari, domin kada yă mutu, gama zan bayyana a cikin girgije a kan murfin.
He said to him/me, “Warn your [older] brother Aaron that he must not enter the Very Holy Place inside the curtain that is in the Sacred Tent whenever he wants to, because the cover of the sacred chest is there. That is the place where the priest (makes atonement for/requests me to forgive) sins. I am present in the cloud that is over the cover of the sacred chest. If Aaron goes in that room when it is not the proper time, he will die!
3 “Ga yadda Haruna zai shiga wuri mai tsarki, zai zo da ɗan bijimi domin hadaya don zunubi da kuma rago domin hadaya ta ƙonawa.
“When Aaron enters the Sacred Tent area, he must bring a bull that [will be killed] to become an offering/sacrifice for sins, and a ram [to be killed] to be an offering that will be completely burned [on the altar].
4 Zai sa toguwar lilin mai tsarki, tare da ɗan ciki na lilin; zai yi ɗamara da igiya kewaye da shi, yă kuma sa hular lilin. Waɗannan su ne riguna masu tsarki; saboda haka dole yă yi wanka kafin yă sa su.
Then he must bathe his whole body, and put on the linen underwear/undershorts and the linen gown. He must tie the linen sash/waistbands around his waist and wrap the turban around his head. Those are his sacred garments.
5 Zai ɗauki bunsurai biyu daga jama’ar Isra’ilawa na hadaya don zunubi da ɗan rago don hadaya ta ƙonawa.
The Israeli people must then bring to him two male goats [to be killed] as an offering/sacrifice for sin, and a ram to be [killed and] burned completely [on the altar].
6 “Haruna zai miƙa bijimi hadaya don zunubinsa yă kuma yi kafara don kansa da gidansa.
“Aaron must offer the bull [to me] to be a sacrifice in order that (I will forgive his sins and the sins of his family/his sins and the sins of his family will be forgiven).
7 Sa’an nan zai ɗauki bunsurai biyu yă miƙa su a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada.
Then he must bring the two male goats to me at the entrance to the Sacred Tent.
8 Haruna zai jefa ƙuri’a don awaki biyun ɗin, ƙuri’a ɗaya domin Ubangiji, ɗayan kuma don azazel
He must (cast lots/throw down stones that have been marked) to determine which goat will be [sacrificed] to me, and which will be the goat that will be set free.
9 Haruna zai kawo akuyar da ƙuri’a ta fāɗi a kai wa Ubangiji yă miƙa ta na hadaya don zunubi.
Aaron must bring to me the goat that was chosen to be sacrificed. It will be an offering for the people’s sins.
10 Amma za a miƙa akuyar da aka zaɓa ta wurin ƙuri’a a matsayi ta azazel da rai a gaban Ubangiji don a yi amfani da ita don kafara ta wurin korinta zuwa cikin jeji kamar azazel.
Aaron must also bring to me the other goat, but it is not to be killed. It will be freed while it is still alive. As a result of Aaron sending it into the desert, the people’s sins will be forgiven.
11 “Haruna zai kawo bijimi domin hadayarsa ta zunubi don yă yi kafara wa kansa da kuma domin gidansa, zai kuma yanka bijimin domin nasa hadaya don zunubi.
“Then Aaron must bring the young bull to me, to be an offering/sacrifice for himself and for his family. He must slaughter that bull to be an offering for their sins, [and he must drain the blood into a basin].
12 Zai ɗauki faranti cike da garwashin wuta daga bagade a gaban Ubangiji, yă kuma cika hannunsa biyu da turare mai ƙanshin da aka niƙa yă kai su bayan labule.
Then he must take some burning coals from the [bronze] altar and put them in the incense burner. Then he must fill his hands with fragrant finely-ground incense. Then he must take the incense and the incense burner inside the curtain into the Very Holy Place [of the Sacred Tent].
13 Zai sa turaren a wuta a gaban Ubangiji, hayaƙin turaren kuwa zai rufe murfin kafarar a bisa Akwatin Alkawari, don kada yă mutu.
There he must put the incense on the burning coals, with the result that a cloud of burning incense will rise up over the lid of the sacred chest. If he obeys these instructions, he will not die [like Korah’s two sons did because of offering incense incorrectly] (OR, [because of being in God’s presence]).
14 Zai ɗibi jinin bijimin da yatsarsa yă yayyafa a gaban murfin kafarar; sa’an nan yă yayyafa jinin da yatsarsa sau bakwai a gaban murfin kafarar.
Then he must dip his finger into [the basin] and sprinkle some blood on the lid of the sacred chest, and also sprinkle some blood seven times against the front of the chest.
15 “Sa’an nan zai yanka akuya na hadaya don zunubi saboda mutane, yă kai jinin bayan labule, yă yi da shi yadda ya yi da jinin bijimin. Zai yayyafa shi a kan murfin kafarar da kuma a gabansa.
[“Aaron must then go outside the Sacred Tent] and slaughter the goat to be an offering for the sins of the people. Then he must bring its blood into the Very Holy Place behind the curtain. There he must sprinkle [some of] that blood on the lid of the sacred chest and against the front of the chest, like he did with the bull’s blood.
16 Ta haka zai yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki saboda ƙazantar tawayen Isra’ilawa, da laifofinsu, da dukan zunubansu. Haka zai yi saboda Tentin Sujada wanda yake a cikinsu a tsakiyar ƙazantarsu.
By doing that, he will purify the Very Holy Place. And he must sprinkle more of the blood on the Sacred Tent, because the tent is in the midst of the camp of the Israeli people who have become unacceptable to me [because of their sins].
17 Kada kowa yă kasance a Tentin Sujada daga lokacin da Haruna ya shiga don yă yi kafara a Wuri Mafi Tsarki har sai ya fita, bayan ya yi kafara domin kansa, gidansa da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
When Aaron goes into the Very Holy Place [in the Sacred Tent] to purify it, no one else is permitted to enter [the other part of] the Sacred Tent. Only after Aaron has performed rituals to enable me to forgive him and his family, and all the Israeli people, is any priest permitted to enter the Sacred Tent.
18 “Sa’an nan zai fita zuwa bagade da yake a gaban Ubangiji, yă yi kafara dominsa. Zai ɗibi jinin bijimi da na akuya yă zuba a ƙahonin bagade.
“Then Aaron must go outside the tent to purify my altar. He must do this by smearing some of the blood from the bull and some of the blood from the goat on each of the projections at the corners of the altar.
19 Zai yayyafa jinin a kan bagade da yatsarsa sau bakwai, yă tsabtacce shi yă kuma tsarkake shi daga ƙazantar Isra’ilawa.
Then Aaron must dip his finger into the [basin of] blood and sprinkle some of the blood over the altar seven times. By doing that, he will cleanse it from being unholy [because of the sins] of the Israeli people, and it will become holy again.
20 “Sa’ad da Haruna ya gama yin kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da kuma bagade, sai yă kawo akuya mai rai.
“When Aaron has finished purifying the Very Holy Place [inside the Sacred Tent] and all of the Sacred Tent and the altar, he must bring the goat that was chosen to be set free.
21 Haruna zai ɗibiya hannuwansa a kan akuya mai ran, yă furta a kansa dukan mugunta da tawayen Isra’ilawa, dukan zunubansu, yă kuma sa su a kan akuyan. Zai kori akuyan zuwa cikin jeji a hannun mutumin da aka ba shi aikin yin haka.
He must put both of his hands on the head of the goat and confess all the sins [DOU] of the Israeli people. By doing that, he will put [the guilt of] their sins on the head of the goat. Then he must give the goat to a man who is chosen, and that man will send the goat out into the desert.
22 Akuyan zai ɗauka a kansa dukan zunubansu zuwa kaɗaitaccen wuri, a can mutumin zai sake shi a jeji.
[It is as though] the goat will carry away into the desert [the guilt for] the sins of all the people.
23 “Sa’an nan Haruna zai shiga Tentin Sujada yă tuɓe rigunansa na lilin da ya sa, kafin yă shiga Wuri Mafi Tsarki, zai kuma bar su a can.
“When Aaron approaches the Sacred Tent, he must take off the linen clothes that he wore when he [previously] entered the Very Holy Place, and he must leave those clothes there.
24 Zai yi wanka a tsattsarkan wuri yă sa rigunarsa na kullum. Sa’an nan zai fita yă miƙa hadaya ta ƙonawa domin kansa da hadaya ta ƙonawa domin mutane, don yă yi kafara domin kansa da kuma domin mutane.
Then he must bathe in a sacred place, put on his regular/ordinary clothes, and sacrifice the animals that will be burned completely on the altar for his own sins and for the sins of the Israeli people. By doing that he will enable me to forgive him and them.
25 Zai kuma ƙone kitsen hadaya don zunubi a kan bagade.
He must also burn on the altar all the fat of the bull and the goat that were sacrificed.
26 “Dole mutumin da ya saki akuya na azazel yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka; bayan haka zai iya shiga sansani.
“The man who was chosen to send the other goat into the desert and free it there must afterwards wash his clothes and bathe. Then he may return to the camp.
27 Dole a ɗauki jini, fata, nama da kuma ƙashin bijimi da akuyan hadaya don zunubi, waɗanda aka kawo jininsu cikin Wuri Mafi Tsarki don kafara, a kai waje da sansani a ƙone.
The carcasses of the bull and the goat that were slaughtered to be an offering/sacrifice for the people’s sins, whose blood was taken inside the Very Holy Place to enable Yahweh to forgive the Israeli people, must be carried outside the camp and burned. The hides/skins of the animals, the inner organs, and the dung must also be burned.
28 Dole mutumin da ya ƙone su yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, bayan haka zai iya shiga sansani.
The man who burns those things must then wash his clothes and bathe before he returns to the camp.
29 “Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare ku. A rana ta goma ga wata na bakwai, dole ku yi mūsu kanku, ba kuwa za ku yi wani aiki ba, ko da mutum baƙo ne a cikinku ko kuwa ɗan ƙasa,
“On (October/the month after the dry season ends), on the day that I have appointed, you all must (fast/abstain from eating food) and not do any work. This is a rule/law that will never end. It must be obeyed by you people who have been Israelis all your lives, and also by foreigners who are living among you.
30 gama a wannan rana za a yi kafara dominku, don a tsarkake ku. Sa’an nan a gaban Ubangiji, za a tsarkake ku daga dukan zunubanku.
On that day, Aaron will perform rituals to enable me to forgive you all, and then I will cleanse/free you all from [the guilt of] all your sins and you will become acceptable to me.
31 Asabbaci ne don hutawa, kuma dole ku yi mūsun kanku; wannan dawwammamiyar farilla ce.
That will be a day for you to rest and not do any work, like the Sabbath days, and you must (fast/abstain from eating food) all that day. That is a permanent command/law for you all to obey.
32 Firist da aka keɓe aka kuma naɗa don yă gāji mahaifinsa a matsayin babban firist ne zai yi kafara. Zai sa rigunan lilin masu tsarki
In future years, [after Aaron has died], this ritual/ceremony to enable me to forgive you all [DOU] will be performed by the Supreme Priest who is anointed [with olive oil] and appointed to serve instead of his ancestor Aaron. He must put on the sacred clothes made of linen
33 yă yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da bagade, da kuma saboda firistoci da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
and offer sacrifices to purify the Very Holy Place, all of the Sacred Tent, the altar, the priests, and all the Israel people [like Aaron did].
34 “Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce gare ku. Za a riƙa yin kafara sau ɗaya a shekara saboda dukan zunuban Isra’ilawa.” Aka kuma yi haka, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
This will be a permanent command/law for you to obey once every year, to enable me to forgive you Israeli people for the sins that you have committed.” Moses/I obeyed all those instructions/commands that Yahweh had given to him/me.