< Firistoci 14 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spoke unto Moses, saying:
2 “Waɗannan su ne ƙa’idodi domin mutumin da yake da cuta a lokacin tsabtaccewarsa, sa’ad da aka kawo shi ga firist.
This shall be the law of the leper in the day of his cleansing: he shall be brought unto the priest.
3 Firist zai fita waje da sansani ya bincike shi. In mutumin ya warke daga cutar fatar jiki mai yaɗuwa,
And the priest shall go forth out of the camp; and the priest shall look, and, behold, if the plague of leprosy be healed in the leper;
4 firist zai umarta a kawo tsuntsaye biyu masu rai, masu tsabta da itacen al’ul, jan ƙyalle da kuma hizzob saboda mutumin da za a tsabtacce.
then shall the priest command to take for him that is to be cleansed two living clean birds, and cedar-wood, and scarlet, and hyssop.
5 Sa’an nan firist zai umarta a kashe ɗaya daga cikin tsuntsayen a bisa ruwa mai kyau a tukunyar laka.
And the priest shall command to kill one of the birds in an earthen vessel over running water.
6 Zai ɗauki tsuntsu mai rai ya tsoma shi tare da itacen al’ul, jan ƙyalle da kuma hizzob cikin jinin tsuntsun da aka yanka a bisa ruwa mai kyau.
As for the living bird, he shall take it, and the cedar-wood, and the scarlet, and the hyssop, and shall dip them and the living bird in the blood of the bird that was killed over the running water.
7 Sau bakwai zai yayyafa wa mutumin da za a tsabtacce daga cutar mai yaɗuwa ya kuma furta shi tsarkakakke. Sa’an nan ya saki tsuntsu mai rai ɗin ya tafi.
And he shall sprinkle upon him that is to be cleansed from the leprosy seven times, and shall pronounce him clean, and shall let go the living bird into the open field.
8 “Dole mutumin da aka tsabtaccen ya wanke rigunansa, ya aske dukan gashinsa ya kuma yi wanka; sa’an nan zai tsabtacce. Bayan wannan zai iya zo cikin sansani, amma dole yă tsaya waje da tentinsa kwana bakwai.
And he that is to be cleansed shall wash his clothes, and shave off all his hair, and bathe himself in water, and he shall be clean; and after that he may come into the camp, but shall dwell outside his tent seven days.
9 A rana ta bakwai ɗin dole yă aske dukan gashinsa; dole yă aske kansa, gemunsa, gashin girarsa da sauran gashinsa. Dole yă wanke rigunansa ya kuma yi wanka, zai kuwa tsabtacce.
And it shall be on the seventh day, that he shall shave all his hair off his head and his beard and his eyebrows, even all his hair he shall shave off; and he shall wash his clothes, and he shall bathe his flesh in water, and he shall be clean.
10 “A rana ta takwas dole yă kawo ɗan rago da’yar tunkiya bana ɗaya, kowane marar lahani, tare da rabin garwan gari mai laushi haɗe da mai domin hadaya ta gari, da kuma moɗa ɗaya na mai.
And on the eighth day he shall take two he-lambs without blemish, and one ewe-lamb of the first year without blemish, and three tenth parts of an ephah of fine flour for a meal-offering, mingled with oil, and one log of oil.
11 Firist da ya furta shi tsarkakakke zai miƙa da wanda za a tsabtaccen da kuma hadayunsa a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada.
And the priest that cleanseth him shall set the man that is to be cleansed, and those things, before the LORD, at the door of the tent of meeting.
12 “Sa’ad da firist zai ɗauki ɗaya daga cikin ragunan ya kuma miƙa shi kamar hadaya don laifi, tare da moɗan mai; zai kaɗa su a gaban Ubangiji kamar hadaya kaɗawa.
And the priest shall take one of the he-lambs, and offer him for a guilt-offering, and the log of oil, and wave them for a wave-offering before the LORD.
13 Zai yanka ɗan ragon a tsattsarkan wuri inda ake yanka hadaya don zunubi da hadaya ta ƙonawa. Gama yadda hadaya ta zunubi ta firist ne, haka hadaya domin laifi ma, hadaya ce mafi tsarki.
And he shall kill the he-lamb in the place where they kill the sin-offering and the burnt-offering, in the place of the sanctuary; for as the sin-offering is the priest's, so is the guilt-offering; it is most holy.
14 Firist ɗin zai ɗiba jinin hadaya don laifin ya zuba a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsabtacce, a babbar yatsar hannunsa na dama a kuma a babbar yatsar ƙafa damansa.
And the priest shall take of the blood of the guilt-offering, and the priest shall put it upon the tip of the right ear of him that is to be cleansed, and upon the thumb of his right hand, and upon the great toe of his right foot.
15 Firist ɗin zai ɗiba daga moɗan mai ɗin ya zuba a tafin hannunsa na hagu,
And the priest shall take of the log of oil, and pour it into the palm of his own left hand.
16 ya tsoma yatsarsa ta dama cikin man da yake a tafin hannunsa, kuma da yatsar zai yayyafa man a gaban Ubangiji sau bakwai.
And the priest shall dip his right finger in the oil that is in his left hand, and shall sprinkle of the oil with his finger seven times before the LORD.
17 Firist zai sa sauran mai da yake cikin tafinsa a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsabtacce, a babbar yatsarsa na dama da kuma a babbar yatsar ƙafarsa ta dama, a bisa jinin hadaya don laifin.
And of the rest of the oil that is in his hand shall the priest put upon the tip of the right ear of him that is to be cleansed, and upon the thumb of his right hand, and upon the great toe of his right foot, upon the blood of the guilt-offering.
18 Sauran man a tafin hannunsa firist zai sa a kan wanda za a tsabtaccen ya kuma yi kafara dominsa a gaban Ubangiji.
And the rest of the oil that is in the priest's hand he shall put upon the head of him that is to be cleansed; and the priest shall make atonement for him before the LORD.
19 “Sa’an nan firist ɗin zai miƙa hadaya don zunubi ya kuma yi kafara saboda wannan da za a tsabtacce daga rashin tsarkinsa. Bayan haka, firist zai yanka hadaya ta ƙonawa
And the priest shall offer the sin-offering, and make atonement for him that is to be cleansed because of his uncleanness; and afterward he shall kill the burnt-offering.
20 ya miƙa ta a bagade, tare da hadaya ta gari, ya kuma yi kafara dominsa, zai kuwa tsabtacce.
And the priest shall offer the burnt-offering and the meal-offering upon the altar; and the priest shall make atonement for him, and he shall be clean.
21 “In kuwa mutumin matalauci ne ba zai iya samu waɗannan ba, to, dole yă ɗauki ɗan rago guda kamar hadaya don laifi a kaɗa don a yi kafara dominsa, tare da humushin garwa gari mai laushi haɗe da mai don hadaya ta gari, da moɗa na mai,
And if he be poor, and his means suffice not, then he shall take one he-lamb for a guilt-offering to be waved, to make atonement for him, and one tenth part of an ephah of fine flour mingled with oil for a meal-offering, and a log of oil;
22 da kurciyoyi biyu ko tattabarai biyu, wanda zai iya samu, ɗaya domin hadaya don zunubi ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa.
and two turtle-doves, or two young pigeons, such as his means suffice for; and the one shall be a sin-offering, and the other a burnt-offering.
23 “A rana ta takwas dole yă kawo su domin tsabtaccewarsa ga firist a ƙofar Tentin Sujada, a gaban Ubangiji.
And on the eighth day he shall bring them for his cleansing unto the priest, unto the door of the tent of meeting, before the LORD.
24 Firist zai ɗauki ɗan rago na hadaya don laifi tare da moɗa na mai, ya kaɗa su a gaban Ubangiji kamar hadaya ta kaɗawa.
And the priest shall take the lamb of the guilt-offering, and the log of oil, and the priest shall wave them for a wave-offering before the LORD.
25 Zai yanka ɗan rago domin hadaya don laifi ya kuma ɗibi jinin ya sa a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsabtaccen, a babban yatsar hannun damansa da kuma a babban yatsar ƙafarsa na dama.
And he shall kill the lamb of the guilt-offering, and the priest shall take of the blood of the guilt-offering, and put it upon the tip of the right ear of him that is to be cleansed, and upon the thumb of his right hand, and upon the great toe of his right foot.
26 Firist zai zuba man a tafin hannunsa na hagu,
And the priest shall pour of the oil into the palm of his own left hand.
27 da yatsarsa na dama zai yayyafa man daga tafinsa sau bakwai a gaban Ubangiji.
And the priest shall sprinkle with his right finger some of the oil that is in his left hand seven times before the LORD.
28 Daga cikin man da yake a tafinsa zai zuba a wuri da ya zuba jinin hadaya don laifi, a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsabtaccen, a babban yatsar hannun damansa da kuma a babban yatsar ƙafa damansa.
And the priest shall put of the oil that is in his hand upon the tip of the right ear of him that is to be cleansed, and upon the thumb of his right hand, and upon the great toe of his right foot, upon the place of the blood of the guilt-offering.
29 Sauran man da yake cikin tafinsa firist ɗin zai zuba a kan wannan da za a tsabtaccen don a yi kafara dominsa a gaban Ubangiji.
And the rest of the oil that is in the priest's hand he shall put upon the head of him that is to be cleansed, to make atonement for him before the LORD.
30 Sa’an nan zai miƙa kurciyoyi ko tattabarai, waɗanda mutumin zai iya,
And he shall offer one of the turtle-doves, or of the young pigeons, such as his means suffice for;
31 ɗaya kamar hadaya don zunubi ɗayan kuma kamar hadaya ta ƙonawa, tare da hadaya ta gari. Ta haka firist zai yi kafara a gaban Ubangiji a madadin wanda za a tsabtacce.”
even such as his means suffice for, the one for a sin-offering, and the other for a burnt-offering, with the meal-offering; and the priest shall make atonement for him that is to be cleansed before the LORD.
32 Waɗannan su ne ƙa’idodi domin mutumin da yake da cutar fatar jiki wanda kuma ba zai iya samun abubuwan hadaya ta kullum domin tsabtaccewarsa ba.
This is the law of him in whom is the plague of leprosy, whose means suffice not for that which pertaineth to his cleansing.
33 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And the LORD spoke unto Moses and unto Aaron, saying:
34 “Sa’ad da kuka shiga ƙasar Kan’ana, wadda nake ba ku kamar gādonku, na kuma sa yaɗuwa cutar fatar jiki a riga a cikin gida a wannan ƙasa,
When ye are come into the land of Canaan, which I give to you for a possession, and I put the plague of leprosy in a house of the land of your possession;
35 dole maigidan ya tafi ya faɗa wa firist ya ce, ‘Na ga wani abu da ya yi kamar cutar fatar jikin da take a riga a cikin gidana.’
then he that owneth the house shall come and tell the priest, saying: 'There seemeth to me to be as it were a plague in the house.'
36 Firist zai umarci a fitar da kome a gidan kafin ya shiga ya bincike cutar fatar jiki da take a rigar, saboda babu abin da yake gidan da za a furta marar tsarki ne. Bayan haka firist zai shiga ya dudduba gidan.
And the priest shall command that they empty the house, before the priest go in to see the plague, that all that is in the house be not made unclean; and afterward the priest shall go in to see the house.
37 Zai bincike cutar fatar jiki da take a riga a bangaye, in kuma yana da tabon kore-kore ko ja-ja da suka bayyana da suka yi zurfi fiye da saman bangon,
And he shall look on the plague, and, behold, if the plague be in the walls of the house with hollow streaks, greenish or reddish, and the appearance thereof be lower than the wall;
38 firist ɗin zai fita a bakin ƙofar gidan ya rufe ta na kwana bakwai.
then the priest shall go out of the house to the door of the house, and shut up the house seven days.
39 A rana ta bakwai ɗin firist zai dawo don yă dudduba gidan. In cutar fatar jiki da take a riga ta yaɗu a bangayen,
And the priest shall come again the seventh day, and shall look; and, behold, if the plague be spread in the walls of the house;
40 zai umarta a ciccire duwatsun da suke da cutar a zubar a wuri marar tsarki waje da birnin.
then the priest shall command that they take out the stones in which the plague is, and cast them into an unclean place without the city.
41 Dole yă sa a kankare duka shafen bangon cikin gidan a kuma zuba kayan da aka kankare a wurin marar tsarki waje da birnin.
And he shall cause the house to be scraped within round about, and they shall pour out the mortar that they scrape off without the city into an unclean place.
42 Sai su ɗebi waɗansu duwatsu su sa a wuraren da suka ciccire waɗancan, su kuma ɗiba sabon laka su yi shafen gidan.
And they shall take other stones, and put them in the place of those stones; and he shall take other mortar, and shall plaster the house.
43 “In cutar fatar jiki da take ta rigar ta sāke bayyana a gidan bayan an ciccire duwatsu aka kankare gidan aka kuma yi shafe,
And if the plague come again, and break out in the house, after that the stones have been taken out, and after the house hath been scraped, and after it is plastered;
44 firist zai je ya bincika shi, in kuwa cutar ta bazu a gidan, to, muguwar cuta ce; gidan marar tsarki ne.
then the priest shall come in and look; and, behold, if the plague be spread in the house, it is a malignant leprosy in the house: it is unclean.
45 Dole a rushe gidan, a fid da duwatsun, katakai da kuma dukan shafen daga birnin zuwa wuri marar tsarki.
And he shall break down the house, the stones of it, and the timber thereof, and all the mortar of the house; and he shall carry them forth out of the city into an unclean place.
46 “Duk wanda ya shiga gidan yayinda aka rufe shi zai ƙazantu har yamma.
Moreover he that goeth into the house all the while that it is shut up shall be unclean until the even.
47 Duk wanda ya kwana ko ya ci abinci a gidan dole yă wanke rigunansa.
And he that lieth in the house shall wash his clothes; and he that eateth in the house shall wash his clothes.
48 “Amma in firist ya zo ya bincika gidan kuma cutar fatar jiki da take ta rigar ba tă bazu ba bayan an yi wa gidan shafe, zai furta gidan tsarkakakke, domin cutar ta tafi.
And if the priest shall come in, and look, and, behold, the plague hath not spread in the house, after the house was plastered; then the priest shall pronounce the house clean, because the plague is healed.
49 Don a tsabtacce gidan, zai ɗauki tsuntsaye biyu da itacen al’ul, jan ƙyalle da hizzob.
And he shall take to cleanse the house two birds, and cedar-wood, and scarlet, and hyssop.
50 Zai yanka ɗaya daga cikin tsuntsayen a bisa ruwa mai kyau a cikin tukunyar laka.
And he shall kill one of the birds in an earthen vessel over running water.
51 Sa’an nan zai ɗauki itacen al’ul, hizzob, jan ƙyalle da kuma tsuntsu mai ran ya tsoma su cikin jinin tsuntsun da aka yanka da kuma cikin ruwa mai kyau, ya yayyafa wa gida sau bakwai.
And he shall take the cedar-wood, and the hyssop, and the scarlet, and the living bird, and dip them in the blood of the slain bird, and in the running water, and sprinkle the house seven times.
52 Zai tsabtacce gidan da jinin tsuntsun, ruwa mai kyau, tsuntsu mai ran, itacen al’ul, hizzob da kuma jan ƙyalle.
And he shall cleanse the house with the blood of the bird, and with the running water, and with the living bird, and with the cedar-wood, and with the hyssop, and with the scarlet.
53 Sa’an nan zai saki tsuntsu mai rai ɗin a fili waje da birnin ya tafi. Ta haka zai yi kafara saboda gidan, gidan kuwa zai zama tsarkakakke.”
But he shall let go the living bird out of the city into the open field; so shall he make atonement for the house; and it shall be clean.
54 Waɗannan su ne ƙa’idodi saboda duk wani cuta mai yaɗuwa, don ƙaiƙayi,
This is the law for all manner of plague of leprosy, and for a scall;
55 don cutar fatar jiki da take a riga ko a cikin gida,
and for the leprosy of a garment, and for a house;
56 da kuma don kumburi, ɓamɓaroki ko tabo,
and for a rising, and for a scab, and for a bright spot;
57 don a tabbatar sa’ad da wani abu mai tsarki da marar tsarki. Waɗannan su ne ƙa’idodi domin cutar fatar jiki mai yaɗuwa da cutar fatar jikin da take a riga.
to teach when it is unclean, and when it is clean; this is the law of leprosy.

< Firistoci 14 >