< Firistoci 10 >

1 ’Ya’yan Haruna maza, Nadab da Abihu suka ɗauki farantansu, suka sa wuta a ciki, suka zuba turare a kai; suka kuma miƙa haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji, ba irin wadda Ubangiji ya umarta ba.
[Two of] Aaron’s sons, Nadab and Abihu, took the pans in which they burned incense. They put some burning coals in them and put incense on top of the coals, but this fire was not acceptable [to Yahweh] because it was not the kind that he had commanded them to burn.
2 Sai wuta ta fito daga Ubangiji ta cinye su, suka kuma mutu a gaban Ubangiji.
So suddenly a fire from Yahweh appeared and burned them up [DOU] in the presence of Yahweh.
3 Sai Musa ya ce Haruna, “Ga abin da Ubangiji yake nufi sa’ad da ya ce, “‘A cikin waɗanda suka kusace ni za a tabbata ni mai tsarki ne; a fuskar dukan mutane za a kuwa girmama ni.’” Haruna ya yi shiru.
Then Moses/I said to Aaron, “That is what Yahweh predicted. He said, ‘Those priests who come near to me, I will show them that they must (respect me/treat me as being holy); in the presence of all the people I am the one who must be honored.’” But Aaron said nothing.
4 Sai Musa ya kira Mishayel da Elzafan,’ya’yan Uzziyel kawun Haruna, ya ce musu, “Ku zo nan; ku ɗauki’yan’uwanku waje da sansani, daga gaban wuri mai tsarki.”
Then Moses/I summoned Mishael and Elzaphan, who were the sons of Aaron’s uncle Uzziel, and said to them, “Take [the corpses of] your cousins outside the camp, away from the front of the Sacred Tent.”
5 Sai suka zo suka ɗauke su, suna nan cikin taguwoyinsu, zuwa waje da sansani yadda Musa ya umarta.
So they carried the corpses, which still had their special gowns on, outside the camp, [and buried them].
6 Sa’an nan Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku yage tufafinku, don kada ku mutu. Yin haka zai jawo fushin Ubangiji a kan dukan jama’a. Amma dangoginku, wato, dukan Isra’ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya hallaka da wuta.
Then Moses/I said to Aaron and his [other two] sons Eleazar and Ithamar, “[You are sad because Nadab and Abihu died, but you must act like you always do]. Do not allow the hair on your [heads] to remain uncombed, and do not tear your clothes. But your relatives and all your fellow Israelis are allowed to mourn for those whom Yahweh destroyed by fire.
7 Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada ko kuwa ku mutu, domin man Shafan Ubangiji yana kanku.” Saboda haka suka yi kamar yadda Musa ya faɗa.
But you must not leave the entrance of the Sacred Tent [to join those who are mourning], because if you do that, you also will die, and Yahweh will punish [MTY] all the people of Israel. Do not forget that Yahweh has set you apart [MTY] to work for him here, [and he does not want you to become defiled by touching a corpse].” So they did what Moses/I told them to do.
8 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana da Haruna ya ce,
Then Yahweh said to Aaron,
9 “Kai da’ya’yanka maza, ba za ku sha ruwan inabi ko wani abu mai sa jiri ba a duk sa’ad da za ku shiga cikin Tentin Sujada, in ba haka ba za ku mutu. Wannan dawwammamiyar farilla ce wa tsararraki masu zuwa.
“You and your [two] sons [who are still alive] must not drink wine or other fermented drinks before you enter the Sacred Tent; if you do that, you will die. That is a command that you and your descendants must obey forever.
10 Dole ku bambanta tsakanin mai tsarki da marar tsarki, tsakanin marar tsabta da mai tsabta,
You must do that in order to learn what things are holy and what things are (not holy/common), and [from the things that are not holy] you must learn what things are acceptable to me and what things are not.
11 za ku kuma koyar da Isra’ilawa dukan farillan da Ubangiji ya ba su ta wurin Musa.”
And you must teach to the Israeli people all the laws that I gave to the Israeli people by telling them to Moses.”
12 Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza da suka ragu, “Ku ɗauki ragowar hadaya ta gari wadda aka yi hadaya ta ƙonawa da ita ga Ubangiji ku ci ba tare da yisti ba, a gefen bagaden, gama tsattsarka ne.
Moses/I said to Aaron and his two sons who were still alive, Eleazar and Ithamar, “Take the offering made from grain that is left after a portion of it has been offered to Yahweh to be burned, and eat it alongside the altar. [It should not be eaten elsewhere], because it is very holy.
13 Ku ci shi a tsattsarkan wuri, gama rabonka ne da na’ya’yanka daga cikin hadayun da akan ƙone da wuta ga Ubangiji; gama haka aka umarce ni.
Eat it in a holy place; it is the share for you and your sons from the offerings that were burned; I have commanded that it be your share.
14 Amma kai da’ya’yanka maza da mata za su iya ci ƙirjin da aka kaɗa, da kuma cinyar da aka miƙa. Ku ci su a wuri mai tsabta; an ba da su gare ku da kuma’ya’yanku a matsayin rabo daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa.
But you and your sons and daughters are permitted to eat the breast and the thigh that were lifted up in front of Yahweh. Eat them in any place that is (holy/acceptable to him). They have been given to you and your descendants as your share of the offerings to enable the Israelis to maintain fellowship [with Yahweh].
15 Cinyar da aka miƙa da kuma ƙirjin da aka kaɗa, dole a kawo su tare da ɓangarori kitsen hadayun da aka yi ta wuri wuta, don a kaɗa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa. Wannan zai zama na kullayaumi gare ka da’ya’yanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
The thigh and the breast that were lifted up in front of Yahweh must be brought with the portions of fat to be burned, to be lifted up in his presence. They will be the regular share for you and your descendants, as Yahweh has commanded.”
16 Sa’ad da Musa ya nemi sani game da akuyar hadaya don zunubi, ya kuwa gane cewa an ƙone shi, sai ya yi fushi da Eleyazar da kuma Itamar,’ya’yan Haruna maza da suka ragu, ya kuma yi tambaya,
When Moses/I inquired about the goat that had been sacrificed to enable the people to be forgiven by Yahweh for the sins they had committed, he/I found out that it had been completely burned. So he/I was angry with Eleazar and Ithamar and asked them,
17 “Me ya sa ba ku ci hadaya don zunubi a cikin wuri mai tsarki ba? Mafi tsaki ne; an ba ku ne don a ɗauke laifin jama’a ta wurin yin kafara saboda su a gaban Ubangiji.
“Why did you not eat near the Sacred Tent the meat of the offering for sin? It was very holy, and it was given to you to enable the Israeli people to no longer be guilty for their sins and to be forgiven for their sins.
18 Da yake ba a kai jininsa cikin wuri mai tsarki ba, ya kamata ku ci akuyar a wuri mai tsarki, kamar yadda na umarta.”
Since its blood was not taken into the holy place inside the Sacred Tent, you should have eaten the [meat of] the goat near the Sacred Tent, as I commanded.”
19 Sai Haruna ya amsa wa Musa, “Yau sun miƙa hadayarsu don zunubi da kuma hadayarsu ta ƙonawa a gaban Ubangiji, ga kuma irin waɗannan abubuwa da suka same ni, da a ce na ci hadaya don zunubi yau, da zai yi kyau ke nan a gaban Ubangiji?”
Aaron replied to Moses/me, “Today the people brought to Yahweh their offering to be forgiven for the sins they had committed, and the offering to be completely burned, [and surely that pleased Yahweh], but [think about the terrible thing] that happened to my other two sons! Would [RHQ] Yahweh have been pleased if I had eaten some of the offering to cause the people to become acceptable to God?”
20 Da Musa ya ji haka, sai ya gamsu.
When Moses/I heard that, he/I was satisfied.

< Firistoci 10 >