< Firistoci 1 >

1 Ubangiji ya kira Musa ya yi masa magana daga cikin Tentin Sujada ya ce,
Or le Seigneur appela Moïse, et il lui parla du tabernacle de témoignage, disant:
2 “Yi magana da Isra’ilawa ka ce musu, ‘Duk sa’ad da waninku ya kawo hadaya ga Ubangiji, ku kawo hadayarku ta dabba daga garkenku ta shanu ko kuwa daga tumakinku.
Tu parleras aux enfants d’Israël et tu leur diras: Un homme d’entre vous qui offrira au Seigneur une hostie de bêtes à quatre pieds, c’est-à-dire qui offrira des bœufs et des brebis comme victimes,
3 “‘In hadaya ta ƙonawar daga shanu ne, sai yă miƙa namiji marar lahani. Dole yă kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă zama yardajje ga Ubangiji.
Si son oblation est un holocauste, et de gros bétail, c’est un mâle sans tâche qu’il offrira, à la porte du tabernacle de témoignage, pour fléchir le Seigneur;
4 Zai ɗibiya hannunsa a kan hadaya ta ƙonawar, za a kuwa karɓa a madadinsa don a yi kafara dominsa.
Et il mettra la main sur la tête de l’hostie qui sera acceptable, et servira à son expiation;
5 Zai yanka ɗan bijimin a gaban Ubangiji, Haruna kuwa da’ya’yansa maza firist, za su kawo jinin su kuma yafa shi a kan bagaden a kowane gefe a mashigin Tentin Sujada.
Puis il immolera le veau devant le Seigneur, et les fils d’Aaron, prêtres, en offriront le sang. le répandant autour de l’autel qui est devant la porte du tabernacle;
6 Zai feɗe hadaya ta ƙonawar, yă yayyanka shi gunduwa-gunduwa.
Et, la peau de l’hostie enlevée, ils en couperont les membres par morceaux,
7 ’Ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci za su hura wuta a bagade, su kuma shirya itace a kan wutar.
Ensuite ils mettront du feu sous l’autel, un tas de bois ayant été auparavant disposé;
8 Sa’an nan’ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci za su shirya gunduwa-gunduwar haɗe da kan da kuma kitsen a kan itace mai cin wuta wanda yake a kan bagaden.
Et arrangeant au-dessus les membres coupés, c’est-à-dire, la tête et tout ce qui tient au foie,
9 Zai wanke kayan cikin da kuma ƙafafun da ruwa, firist ɗin kuwa zai ƙone dukan waɗannan a kan bagade. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Les intestins et les pieds ayant été auparavant lavés dans l’eau; puis le prêtre les brûlera sur l’autel en holocauste et en suave odeur pour le Seigneur.
10 “‘In hadaya ta ƙonawar daga garke ne, ko na tumaki, ko na awaki, zai miƙa namiji ne marar lahani.
Que si l’oblation de bêtes à quatre pieds est un holocauste de brebis ou de chèvres, c’est un mâle sans tache qu’il offrira;
11 Zai yanka shi a gefen arewa na bagaden a gaban Ubangiji,’ya’yan Haruna firistoci kuwa za su yayyafa jinin dabbar a bagaden a kowane gefe.
Et il l’immolera au côté de l’autel qui regarde l’aquilon, devant le Seigneur; pour son sang, les fils d’Aaron le répandront sur l’autel tout autour;
12 Zai yanka shi gunduwa-gunduwa, firist kuwa zai shirya su haɗe da kan, da kuma kitsen a kan itace mai cin wutar da yake a kan bagade.
Et ils couperont les membres, la tête et tout ce qui tient au foie, et ils les placeront sur le bois au-dessous duquel doit être mis le feu.
13 Zai wanke kayan cikin da kuma ƙafafun da ruwa, firist ɗin kuwa zai ƙone dukan waɗannan a kan bagade. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Mais les intestins et les pieds, ils les laveront dans l’eau. Et le prêtre brûlera toutes ces choses offertes sur l’autel, en holocauste et en odeur très suave pour le Seigneur.
14 “‘In hadaya ga Ubangiji ɗin, hadaya ta ƙonawa ta tsuntsaye ce, zai miƙa kurciya ko’yar tattabara.
Mais si c’est en oiseaux que se fait l’oblation de l’holocauste au Seigneur: en tourterelles, et petits de colombe,
15 Firist zai kawo ta bagade, yă murɗe wuyan tsuntsun yă ƙone shi a kan bagade; zai tsiyaye jininsa tsuntsun a gefen bagaden.
Le prêtre offrira la victime à l’autel, et lui tournant la tête en arrière sur le cou, et ouvrant une plaie, il fera couler le sang sur le bord de l’autel;
16 Amma zai ɗauki kayan cikin tsuntsun da gashin yă zubar da su a gefen bagaden a wajen gabas a wurin zuba toka.
Mais la vésicule du gosier et les plumes, il les jettera auprès de l’autel, du côté oriental, au lieu dans lequel les cendres ont coutume d’être répandues.
17 Zai tsaga shi biyu a tsaka, amma ba zai raba shi ba. Firist ɗin zai ɗibiya shi a bisa itacen da yake bisa bagaden, yă ƙone shi. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
Il lui rompra les ailes, et il ne la coupera, ni ne la divisera par le fer, mais il la brûlera sur l’autel, le feu ayant été mis sous le bois. C’est un holocauste et une oblation d’une très suave odeur pour le Seigneur.

< Firistoci 1 >