< Makoki 5 >
1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Згадай, Господи, що́ з нами сталося, — зглянься й побач нашу га́ньбу, —
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
наша спа́дщина діста́лась чужим, доми наші — чужи́нцям!
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Поставали ми си́ротами: нема ба́тька, а ма́тінки наші — неначе ті вдо́ви!
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Свою воду за срі́бло ми п'ємо́, наші дро́ва за гроші оде́ржуємо.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
У поти́лицю нас поганяють, помучені ми, і споко́ю не маємо!
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
До Єгипту й Асирії ру́ку витя́гуємо, — щоб наси́титись хлібом!
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Батьки наші грішили, але їх нема, — а ми двигаємо їхні прови́ни!
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Раби запанува́ли над нами, і немає ніко́го, хто б ви́рятував з їхньої руки.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Нара́жуючи свою душу на меч у пустині, достаємо свій хліб.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Шкіра наша, мов піч, — попали́лась з пекучого голоду,
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Жінок на Сіоні безче́стили, дівчат — по Юдейських містах.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Князі їхньою рукою пові́шені, лиця стари́х не пошано́вані.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Юнаки́ носять камінь млино́вий, а хлопці під ношею дров спотика́ються.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Перестали сиді́ти старші́ в брамі, юнаки́ — свою пісню співати,
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
втіха нашого серця спини́лась, наш та́нець змінивсь на жало́бу.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Спа́ла корона у нас з голови́, о горе, бо ми прогріши́лись, —
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
тому́ наше серце боля́ще, тому́ наші очі поте́мніли,
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
через го́ру Сіон, що спусто́шена, бро́дять лисиці по ній.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Пробува́єш Ти, Господи, вічно, Твій престо́л з роду в рід:
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Нащо ж на́с забуваєш навік, покидаєш на довгі дні нас?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Приверни́ нас до Себе, о Господи, — і ве́рнемось ми, віднови́ наші дні, як давні́ше було́!
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Хіба́ Ти цілко́м нас відкинув, прогні́вавсь занадто на нас?