< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
ACUÉRDATE, oh Jehová, de lo que nos ha sucedido: ve y mira nuestro oprobio.
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Nuestra heredad se ha vuelto á extraños, nuestras casas á forasteros.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Huérfanos somos sin padre, nuestras madres como viudas.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Nuestra agua bebemos por dinero; nuestra leña por precio compramos.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Persecución padecemos sobre nuestra cerviz: nos cansamos, y no hay para nosotros reposo.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Al Egipcio y al Asirio dimos la mano, para saciarnos de pan.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Nuestros padres pecaron, y son muertos; y nosotros llevamos sus castigos.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Siervos se enseñorearon de nosotros; no hubo quien de su mano nos librase.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Con peligro de nuestras vidas traíamos nuestro pan delante del cuchillo del desierto.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Nuestra piel se ennegreció como un horno á causa del ardor del hambre.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Violaron á las mujeres en Sión, á las vírgenes en las ciudades de Judá.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
A los príncipes colgaron por su mano; no respetaron el rostro de los viejos.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Llevaron los mozos á moler, y los muchachos desfallecieron en la leña.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Los ancianos cesaron de la puerta, los mancebos de sus canciones.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
Cesó el gozo de nuestro corazón; nuestro corro se tornó en luto.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Cayó la corona de nuestra cabeza: ¡ay ahora de nosotros! porque pecamos.
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Por esto fué entristecido nuestro corazón, por esto se entenebrecieron nuestros ojos:
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
Por el monte de Sión que está asolado; zorras andan en él.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Mas tú, Jehová, permanecerás para siempre: tu trono de generación en generación.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
¿Por qué te olvidarás para siempre de nosotros, y nos dejarás por largos días?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Vuélvenos, oh Jehová, á ti, y nos volveremos: renueva nuestros días como al principio.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Porque repeliendo nos has desechado; te has airado contra nosotros en gran manera.

< Makoki 5 >