< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Opomeni se, Gospode, što nas zadesi; pogledaj i vidi sramotu našu.
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Našljedstvo naše privali se tuðincima, domovi naši inostrancima.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Postasmo sirote, bez oca, matere naše kao udovice.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Svoju vodu pijemo za novce, svoja drva kupujemo.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Na vratu nam je jaram, i gone nas; umoreni nemamo odmora.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Pružamo ruku k Misircima i Asircima, da se nasitimo hljeba.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Oci naši zgriješiše, i nema ih, a mi nosimo bezakonja njihova.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Robovi nam gospodare, nema nikoga da izbavi iz ruku njihovijeh.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Sa strahom za život svoj od maèa u pustinji donosimo sebi hljeb.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Koža nam pocrnje kao peæ od ljute gladi.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Sramote žene na Sionu i djevojke po gradovima Judinijem.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Knezove vješaju svojim rukama, ne poštuju lica staraèkoga.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Mladiæe uzimaju pod žrvnje, i djeca padaju pod drvima.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Staraca nema više na vratima, ni mladiæa na pjevanju.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
Nesta radosti srcu našemu, igra naša pretvori se u žalost.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Pade vijenac s glave naše; teško nama, što zgriješismo!
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Stoga je srce naše žalosno, stoga oèi naše potamnješe,
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
Sa gore Siona, što opustje, i lisice idu po njoj.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Ti, Gospode, ostaješ dovijeka, prijesto tvoj od koljena do koljena.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Zašto hoæeš da nas zaboraviš dovijeka, da nas ostaviš zadugo?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Obrati nas, Gospode, k sebi, i obratiæemo se; ponovi dane naše kako bijahu prije.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Jer eda li æeš nas sasvijem odbaciti i gnjeviti se na nas veoma?

< Makoki 5 >