< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
ای یهوه آنچه بر ما واقع شد به یاد آور وملاحظه فرموده، عار ما را ببین.۱
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
میراث ما از آن غریبان و خانه های ما از آن اجنبیان گردیده است.۲
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
ما یتیم و بی‌پدر شده‌ایم و مادران ما مثل بیوه‌ها گردیده‌اند.۳
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
آب خود را به نقره می‌نوشیم و هیزم ما به مافروخته می‌شود.۴
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
تعاقب کنندگان ما به گردن ما رسیده‌اند وخسته شده، راحت نداریم.۵
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
با اهل مصر و آشور دست دادیم تا از نان سیرشویم.۶
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
پدران ما گناه ورزیده، نابود شده‌اند و مامتحمل عصیان ایشان گردیده‌ایم.۷
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
غلامان بر ما حکمرانی می‌کنند و کسی نیست که از دست ایشان رهایی دهد.۸
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
از ترس شمشیر اهل بیابان، نان خود را بخطرجان خویش می‌یابیم.۹
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
پوست ما به‌سبب سموم قحط مثل تنورسوخته شده است.۱۰
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
زنان را در صهیون بی‌عصمت کردند ودوشیزگان را در شهرهای یهودا.۱۱
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
سروران از دست ایشان به دار کشیده شده و به مشایخ اعتنا ننمودند.۱۲
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
جوانان سنگهای آسیا را برمی دارند وکودکان زیر بار هیزم می‌افتند.۱۳
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
مشایخ از دروازه‌ها نابود شدند و جوانان ازنغمه سرایی خویش.۱۴
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
شادی دل ما نیست شد و رقص ما به ماتم مبدل گردید.۱۵
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
تاج از سر ما افتاد، وای بر ما زیرا که گناه کردیم.۱۶
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
از این جهت دل ما بیتاب شده است و به‌سبب این چیزها چشمان ما تار گردیده است.۱۷
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
یعنی به‌خاطر کوه صهیون که ویران شد وروباهان در آن گردش می‌کنند.۱۸
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
اما تو‌ای یهوه تا ابدالاباد جلوس می‌فرمایی و کرسی تو تا جمیع دهرها خواهدبود.۱۹
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
پس برای چه ما را تا به ابد فراموش کرده وما را مدت مدیدی ترک نموده‌ای.۲۰
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
‌ای یهوه ما را بسوی خود برگردان وبازگشت خواهیم کرد و ایام ما را مثل زمان سلف تازه کن.۲۱
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
و الا ما را بالکل رد نموده‌ای و بر مابی نهایت غضبناک شده‌ای.۲۲

< Makoki 5 >