< Makoki 5 >
1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
主よ、われわれに臨んだ事を覚えてください。われわれのはずかしめを顧みてください。
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
われわれの嗣業は他国の人に移り、家は異邦人のものとなった。
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
われわれはみなしごとなって父はなく、母はやもめにひとしい。
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
われわれは金を出して水を飲み、価を払って、たきぎを獲なければならない。
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
われわれは首にくびきをかけられて追い使われ、疲れても休むことができない。
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
われわれは足りるだけの食物を獲るために、エジプトおよびアッスリヤに手をさし伸べた。
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
われわれの先祖は罪を犯して、すでに世になく、われわれはその不義の責めを負っている。
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
奴隷であった者がわれわれを治めるが、われわれをその手から救い出す者がない。
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
われわれは荒野のつるぎのゆえに、おのが命をかけて食物を獲る。
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
われわれの皮膚は飢餓の激しい熱のために、炉のように熱い。
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
女たちはシオンで犯され、おとめたちはユダの町々で汚された。
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
君たる者も彼らの手でつるされ、長老たちも尊ばれず、
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
若者たちは、ひきうすをになわせられ、わらべたちは、たきぎを負って、よろめき、
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
長老たちは門に集まることをやめ、若者たちはその音楽を廃した。
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
われわれの心の喜びはやみ、踊りは悲しみに変り、
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
われわれの冠はこうべから落ちた。わざわいなるかな、われわれは罪を犯したからである。
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
このために、われわれの心は衰え、これらの事のために、われわれの目はくらくなった。
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
シオンの山は荒れはて、山犬がその上を歩いているからである。
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
しかし主よ、あなたはとこしえに統べ治められる。あなたの、み位は世々絶えることがない。
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
なぜ、あなたはわれわれをながく忘れ、われわれを久しく捨ておかれるのですか。
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
主よ、あなたに帰らせてください、われわれは帰ります。われわれの日を新たにして、いにしえの日のようにしてください。
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
あなたは全くわれわれを捨てられたのですか、はなはだしく怒っていられるのですか。