< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Gedenke, HERR, dessen, was uns widerfahren ist! Blicke her und sieh unsere Schmach!
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Unser Erbbesitz ist an Fremde übergegangen, unsere Häuser an Ausländer.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Waisen sind wir geworden, vaterlos, unsere Mütter sind wie Witwen.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Unser Wasser trinken wir um Geld, nur gegen Zahlung erhalten wir unser eignes Holz.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Unsere Verfolger sitzen uns auf dem Nacken, und sind wir ermattet, gönnt man uns keine Ruhe.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Den Ägyptern haben wir die Hand gereicht und den Assyrern, um uns satt zu essen. –
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Unsere Väter, die gesündigt haben, sind nicht mehr: wir müssen ihre Verschuldungen büßen.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Knechte herrschen über uns: niemand entreißt uns ihrer Hand.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Mit Lebensgefahr schaffen wir unser Brot herein, in Angst vor dem Schwert der Wüstenbewohner.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Unsere Haut glüht wie ein Ofen von der Fieberglut des Hungers.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Ehefrauen haben sie in Zion geschändet, Jungfrauen in den Städten Judas.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Fürsten sind von ihrer Hand gehenkt worden, das Ansehn der Ältesten wird nicht geachtet.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Jünglinge müssen die Handmühle schleppen, und Knaben wanken unter Lasten von Holz.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Die Alten bleiben fern vom Stadttor, die Jungen von ihrem Saitenspiel.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
Geschwunden ist die Freude unsers Herzens, unser Reigentanz hat sich in Trauer verwandelt.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Die Krone ist uns vom Haupt gefallen: wehe uns, daß wir gesündigt haben!
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Darob ist unser Herz krank geworden, darüber sind unsere Augen umdüstert:
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
über den Zionsberg, der verödet daliegt, auf dem die Füchse ihr Wesen treiben.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Du aber, HERR, thronst in Ewigkeit, dein Herrscherstuhl steht fest von Geschlecht zu Geschlecht.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Warum willst du uns vergessen für immer, uns verlassen lebenslang?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Führe uns, HERR, zu dir zurück, daß wir umkehren! Laß unsere Tage erneuert werden wie vor alters!
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Oder hast du uns gänzlich verworfen? Zürnst du uns unversöhnlich?

< Makoki 5 >