< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Gedenke, HERR, wie es uns gehet; schau und siehe an unsere Schmach!
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Unser Erbe ist den Fremden zuteil worden und unsere Häuser den Ausländern.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Wir sind Waisen und haben keinen Vater; unsere Mütter sind wie Witwen.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Unser eigen Wasser müssen wir um Geld trinken; unser Holz muß man bezahlt bringen lassen.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Man treibt uns über Hals, und wenn wir schon müde sind, läßt man uns doch keine Ruhe.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Wir haben uns müssen Ägypten und Assur ergeben, auf daß wir doch Brot satt zu essen haben.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Unsere Väter haben gesündiget und sind nicht mehr vorhanden; und wir müssen ihre Missetat entgelten.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Knechte herrschen über uns, und ist niemand, der uns von ihrer Hand errette.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Wir müssen unser Brot mit Fahr unsers Lebens holen vor dem Schwert in der Wüste.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Unsere Haut ist verbrannt wie in einem Ofen vor dem greulichen Hunger.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Sie haben die Weiber zu Zion geschwächt und die Jungfrauen in den Städten Judas.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Die Fürsten sind von ihnen gehenket, und die Person der Alten hat man nicht geehret.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Die Jünglinge haben Mühlsteine müssen tragen und die Knaben über dem Holztragen straucheln.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Es sitzen die Alten nicht mehr unter dem Tor, und die Jünglinge treiben kein Saitenspiel mehr.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
Unsers Herzens Freude hat ein Ende, unser Reigen ist in Wehklagen verkehret.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Die Krone unsers Haupts ist abgefallen. O wehe, daß wir so gesündiget haben!
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Darum ist auch unser Herz betrübt, und unsere Augen sind finster worden
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
um des Berges Zions willen, daß er so wüst liegt, daß die Füchse darüberlaufen.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Aber du, HERR, der du ewiglich bleibest und dein Thron für und für,
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
warum willst du unser so gar vergessen und uns die Länge so gar verlassen?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Bringe uns, HERR, wieder zu dir, daß wir wieder heimkommen; verneue unsere Tage wie vor alters!
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Denn du hast uns verworfen und bist allzusehr über uns erzürnet.

< Makoki 5 >