< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Souviens-toi, ô Eternel! de ce qui nous est arrivé; regarde et vois notre opprobre.
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Notre héritage a été renversé par des étrangers, nos maisons par des forains.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Nous sommes devenus [comme] des orphelins qui sont sans pères, et nos mères sont comme des veuves.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Nous avons bu notre eau pour de l’argent, et notre bois nous a été mis à prix.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Nous avons été poursuivis l’épée sur la gorge. Nous nous sommes donnés beaucoup de mouvement, [et] nous n’avons point eu de repos.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Nous avons étendu la main aux Egyptiens [et] aux Assyriens pour avoir suffisamment de pain.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Nos pères ont péché, et ne sont plus; [et] nous avons porté leurs iniquités.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Les esclaves ont dominé sur nous, [et] personne ne nous a délivrés de leurs mains.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Nous amenions notre pain au péril de notre vie, à cause de l’épée du désert.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Notre peau a été noircie comme un four, à cause de l’ardeur véhémente de la faim.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Ils ont humilié les femmes dans Sion, et les vierges dans les villes de Juda.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Les principaux ont été pendus par leur main; et on n’a porté aucun respect à la personne des Anciens.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Ils ont pris les jeunes gens pour moudre, et les enfants sont tombés sous le bois.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Les Anciens ont cessé de se trouver aux portes, et les jeunes gens de chanter.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
La joie de notre cœur est cessée, et notre danse est tournée en deuil.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
La couronne de notre tête est tombée. Malheur maintenant à nous parce que nous avons péché!
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
C’est pourquoi notre cœur est languissant. A cause de ces choses nos yeux sont obscurcis.
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
A cause de la montagne de Sion qui est désolée; les renards n’en bougent point.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
[Mais] toi, ô Eternel! tu demeures éternellement, et ton trône est d’âge en âge.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Pourquoi nous oublierais-tu à jamais? pourquoi nous délaisserais-tu si longtemps?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Convertis-nous à toi, ô Eternel! et nous serons convertis; renouvelle nos jours comme ils étaient autrefois.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Mais tu nous as entièrement rejetés, tu t’es extrêmement courroucé contre nous.

< Makoki 5 >