< Makoki 5 >
1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Souviens-toi, ô Eternel, de ce qui nous est advenu; regarde et vois notre opprobre!
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Notre héritage a passé à des étrangers, nos maisons à des gentils.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Nous sommes devenus des orphelins, privés de père; nos mères sont pareilles à des veuves.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Notre eau, nous ne pouvons 'la boire qu’à prix d’argent; notre bois, nous n’en disposons qu’en l’achetant.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
On nous poursuit l’épée dans les reins; nous sommes à bout de forces: point de répit pour nous!
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
En Egypte nous avons tendu la main, et à Achour, pour avoir du pain en suffisance.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Nos pères avaient péché: ils ne sont plus, et nous portons le poids de leurs fautes.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Des esclaves ont pris le dessus sur nous: personne ne nous soustrait à leur pouvoir.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Au péril de notre vie nous nous procurons nos vivres, le glaive sévissant au désert.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Notre peau est brûlante comme un four, par suite de la fièvre desséchante de la faim.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
On a violenté des femmes dans Sion, des vierges dans les villes de Juda.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Des princes ont été pendus par leurs mains; on n’a témoigné nul égard pour la personne des vieillards.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Les adolescents ont dû porter la meule, les jeunes gens ont trébuché, sous le faix des bûches.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Les vieillards ont cessé de paraître à la Porte, les jeunes gens d’entonner leurs chansons.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
Toute joie est bannie de notre cœur; nos danses joyeuses sont changées en deuil.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Elle est tombée, la couronne de notre tête; malheur à nous, parce que nous avons péché!
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Ce qui nous déchire le cœur, ce qui obscurcit nos yeux,
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
c’est de voir le mont Sion en ruines, foulé par les renards.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Toi, ô Eternel, qui sièges immuable, dont le trône subsiste d’âge en âge,
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
pourquoi nous oublies-tu si obstinément, nous délaisses-tu de si longs jours?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Ramène-nous vers toi, ô Eternel, nous voulons te revenir; renouvelle pour nous les jours d’autrefois.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Se peut-il que tu nous aies complètement rejetés et que tu nourrisses contre nous une colère inexorable? Ramène-nous vers toi, ô Eternel, nous voulons te revenir; renouvelle pour nous les jours d’autrefois.