< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Remember O Yahweh what? has it happened to us (look! *Q(K)*) and see reproach our.
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Inheritance our it has been turned over to strangers houses our to foreigners.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Fatherless ones we have become (and there not *Q(K)*) [is] a father mothers our [are] like widows.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Water our for money we have drunk wood our for a price they come.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
At neck our we have been pursued we have become weary (and not *Q(K)*) it has been given rest to us.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Egypt we have given a hand Assyria to be satisfied bread.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Ancestors our they sinned (and not [are] they and we *Q(K)*) iniquities their we have borne.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Slaves they have ruled over us [is one who] rescues there not from hand their.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
With life our we bring bread our because of [the] sword of the wilderness.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Skin our like an oven they have grown hot because of [the] burning heat of hunger.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Women in Zion men have humiliated virgins in [the] cities of Judah.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Princes by hand their they have been hanged [the] face of elders not they have been honored.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Young men a mill they have lifted and young men with wood they have staggered.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Old [men] from [the] gate they have ceased young men from music their.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
It has ceased [the] joy of heart our it has been changed into mourning dancing our.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
It has fallen [the] crown of head our woe! please to us for we have sinned.
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
On this it has become faint heart our on these [things] they have grown dim eyes our.
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
On [the] mountain of Zion that [is] desolate foxes they have prowled on it.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
You O Yahweh for ever you will sit throne your [is] to a generation and a generation.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Why? to perpetuity do you forget us do you abandon? us for length of days.
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Cause to return us O Yahweh - to yourself (so let us return *Q(K)*) renew days our like ancient time.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
That except certainly you have rejected us you are angry towards us up to muchness.

< Makoki 5 >