< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Remember, O Lord, what hath occurred to us, look down, and behold our disgrace.
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Our inheritance is turned over to strangers, our houses to aliens.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Orphans are we become, and [we are] without a father, our mothers are like widows.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Our water have we drunk for money: our wood cometh to us for a purchase price.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Up to our necks are we pursued: we are fatigued, and no rest is allowed us.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
To Egypt do we stretch out our hand, to Asshur, to be satisfied with bread.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Our fathers have sinned, and are no more; but we have indeed to bear their iniquities.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Servants rule over us: no one delivereth us out of their hand.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
At the peril of our life must we bring home our bread, because of the sword of the wilderness.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Our skin gloweth like an oven, because of the heat of famine.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Women have they ravished in Zion, virgins, in the cities of Judah.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Princes were hanged up by their hand: the faces of elders were not honored.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Young men they bore to the mill, and boys stumbled under the wood.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
The elders have ceased from the gate, young men, from their singing.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
Ceased hath the joy of our heart: our dance is changed into mourning.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Fallen is the crown of our head: woe to us, for we have sinned.
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Because of this is our heart made sick; for these things are our eyes dimmed;
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
Because of the mount of Zion which is wasted, foxes walk about on it.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
O thou, Lord, wilt truly abide for ever, thy throne existeth throughout all generations.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Wherefore wilt thou forget us for ever! wilt thou forsake us for so long a time?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Cause us to return, O Lord, unto thee, and we will return: renew our days as of old.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
For wouldst thou entirely reject us, be wroth with us to the uttermost?

< Makoki 5 >