< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Remember, O Lord, what is come vpon vs: consider, and behold our reproche.
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Our inheritance is turned to the strangers, our houses to the aliants.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
We are fatherles, euen without father, and our mothers are as widowes.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Wee haue drunke our water for money, and our wood is solde vnto vs.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Our neckes are vnder persecution: we are wearie, and haue no rest.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
We haue giuen our handes to the Egyptians, and to Asshur, to be satisfied with bread.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Our fathers haue sinned, and are not, and we haue borne their iniquities.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Seruants haue ruled ouer vs, none would deliuer vs out of their hands.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Wee gate our bread with the perill of our liues, because of the sword of the wildernesse.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Our skinne was blacke like as an ouen because of the terrible famine.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
They defiled the women in Zion, and the maydes in the cities of Iudah.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
The princes are hanged vp by their hande: the faces of the elders were not had in honour.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
They tooke the yong men to grinde, and the children fell vnder the wood.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
The Elders haue ceased from the gate and the yong men from their songs.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
The ioy of our heart is gone, our daunce is turned into mourning.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
The crowne of our head is fallen: wo nowe vnto vs, that we haue sinned.
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Therefore our heart is heauy for these things, our eyes are dimme,
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
Because of the mountaine of Zion which is desolate: the foxes runne vpon it.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
But thou, O Lord, remainest for euer: thy throne is from generation to generation.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Wherefore doest thou forget vs for euer, and forsake vs so long time?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Turne thou vs vnto thee, O Lord, and we shalbe turned: renue our dayes as of olde.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
But thou hast vtterly reiected vs: thou art exceedingly angry against vs.

< Makoki 5 >