< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Gedenk, HEERE, wat ons geschied is, aanschouw het, en zie onzen smaad aan.
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Ons erfdeel is tot de vreemdelingen gewend, onze huizen tot de uitlanders.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Wij zijn wezen zonder vader, onze moeders zijn als de weduwen.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Ons water moeten wij voor geld drinken; ons hout komt ons op prijs te staan.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Wij lijden vervolging op onze halzen; zijn wij woede, men laat ons geen rust.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Wij hebben den Egyptenaar de hand gegeven, en den Assyrier, om met brood verzadigd te worden.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Onze vaders hebben gezondigd, en zijn niet meer, en wij dragen hun ongerechtigheden.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Knechten heersen over ons; er is niemand, die ons uit hun hand rukke.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Wij moeten ons brood met gevaar onzes levens halen, vanwege het zwaard der woestijn.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Onze huid is zwart geworden gelijk een oven, vanwege den geweldigen storm des hongers.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Zij hebben de vrouwen te Sion verkracht, en de jonge dochters in de steden van Juda.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
De vorsten zijn door hunlieder hand opgehangen; de aangezichten der ouden zijn niet geeerd geweest.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Zij hebben de jongelingen weggenomen, om te malen, en de jongens struikelen onder het hout.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
De ouden houden op van de poort, de jongelingen van hun snarenspel.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
De vreugde onzes harten houdt op, onze rei is in treurigheid veranderd.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
De kroon onzes hoofds is afgevallen; o wee nu onzer, dat wij zo gezondigd hebben!
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Daarom is ons hart mat, om deze dingen zijn onze ogen duister geworden.
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
Om des bergs Sions wil, die verwoest is, waar de vossen op lopen.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Gij, o HEERE, zit in eeuwigheid, Uw troon is van geslacht tot geslacht.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Waarom zoudt Gij ons steeds vergeten? Waarom zoudt Gij ons zo langen tijd verlaten?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
HEERE, bekeer ons tot U, zo zullen wij bekeerd zijn; vernieuw onze dagen als van ouds.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Want zoudt Gij ons ganselijk verwerpen? Zoudt Gij zozeer tegen ons verbolgen zijn?

< Makoki 5 >