< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
HERRE, kom vor skæbne i Hu, sku ned og se vor skændsel!
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Vor Arvelod tilfaldt fremmede, Udlændinge fik vore Huse.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Forældreløse, faderløse er vi, som Enker er vore Mødre.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Vort Drikkevand må vi købe, betale må vi vort Brænde.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Åget trykker vor Nakke, vi trættes og finder ej Hvile.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Ægypten rakte vi Hånd, Assur, for at mættes med Brød.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Vore Fædre, som synded, er borte, og vi må bære deres Skyld.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Over os råder Trælle, ingen frier os fra dem.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Med Livsfare henter vi vort Brød, udsatte for Ørkenens Sværd.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Vor Hud er sværtet som en Ovn af Hungerens svidende Lue.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
De skændede kvinder i Zion, Jomfruer i Judas Byer.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Fyrster greb de og hængte, tog intet Hensyn til gamle.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Ynglinge sattes til Kværnen, under Brændeknippet segnede Drenge.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
De gamle forsvandt fra Porten, de unge fra Strengenes Leg.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
Vort Hjertes Glæde er borte, vor Dans er vendt til Sorg.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Kronen faldt af vort Hoved, ve os, at vi har syndet!
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Vort Hjerte blev derfor sygt, derfor vort Øje mørkt:
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
For Zions Bjerg, som er øde, Ræve tumler sig der.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Du, HERRE, troner for evigt, fra Slægt til Slægt står din trone.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Hvi glemmer du os bestandig og svigter os alle dage?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Omvend os, HERRE, til dig, så vender vi om, giv os nye Dage, som fordum!
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Eller har du helt stødt os bort, er din Vrede mod os uden Ende?

< Makoki 5 >