< Makoki 5 >
1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Herre! kom i Hu, hvad der er sket os; sku ned og se vor Forhaanelse!
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Vor Arv er gaaet over til fremmede, vore Huse til Udlændinge.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Vi ere blevne faderløse, uden Fader, vore Mødre ere som Enker.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Vandet, vi drikke, købe vi for Penge; vort Brænde kommer til os for Betaling.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Man er os paa Halsen, vi forfølges; vi blive trætte og faa ikke Hvile.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Vi have rakt Haanden imod Ægypten, imod Assyrien for at mættes af Brød.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Vore Fædre have syndet, de ere ikke mere, og vi bære deres Misgerninger.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Trælle herske over os; der er ingen, som frier af deres Haand.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Vi hente vort Brød med Fare for vort Liv, formedelst Sværdet i Ørken.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Vor Hud er forbrændt som en Ovn, af Hungerens Glød.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
De krænke Kvinderne i Zion, Jomfruerne i Judas Stæder.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Fyrster ere hængte af deres Haand, Oldingers Person bliver ikke æret.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Unge Karle maatte tage fat paa Kværnen, og Drenge segnede under Byrden af Ved.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
De Ældste have hørt op med at sidde i Porten, de unge Karle med deres Strengeleg.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
Vort Hjertes Glæde er hørt op, vor Dans er vendt om til Sorrig.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Vort Hoveds Krone er affalden; o ve os! thi vi have syndet.
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Derfor er vort Hjerte sygt, derfor ere vore Øjne formørkede:
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
For Zions Bjergs Skyld, som er øde, Ræve løbe derpaa.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Du, Herre! du bliver evindelig, din Trone fra Slægt til Slægt.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Hvorfor vil du glemme os evindelig? forlade os saa lang en Tid?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Herre! før os tilbage til dig, saa ville vi vende tilbage, forny vore Dage som i fordums Tid!
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Thi mon du aldeles har forkastet os? mon du er saa saare vred paa os?