< Makoki 5 >
1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Rozpomeň se, Hospodine, co se nám děje; popatř a viz pohanění naše.
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Dědictví naše obráceno jest k cizím, domové naši k cizozemcům.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Sirotci jsme a bez otce, matky naše jsou jako vdovy.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Vody své za peníze pijeme, dříví naše za záplatu přichází.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Na hrdle svém protivenství snášíme, pracujeme, nedopouští se nám odpočinouti.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Egyptským podáváme ruky i Assyrským, abychom nasyceni byli chlebem.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Otcové naši hřešili, není jich, my pak trestáni po nich neseme.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Služebníci panují nad námi; není žádného, kdo by vytrhl z ruky jejich.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
S opovážením se života svého hledáme chleba svého, pro strach meče i na poušti.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Kůže naše jako pec zčernaly od náramného hladu.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Ženám na Sionu i pannám v městech Judských násilé činí.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Knížata rukou jejich zvěšena jsou, osoby starých nemají v poctivosti.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Mládence k žernovu berou, a pacholata pod dřívím klesají.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Starci sedati v branách přestali a mládenci od zpěvů svých.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
Přestala radost srdce našeho, obrátilo se v kvílení plésání naše.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Spadla koruna s hlavy naší; běda nám již, že jsme hřešili.
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Protoť jest mdlé srdce naše, pro tyť věci zatměly se oči naše,
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
Pro horu Sion, že zpuštěna jest; lišky chodí po ní.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Ty Hospodine, na věky zůstáváš, a stolice tvá od národu do pronárodu.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Proč se zapomínáš na věky na nás, a opouštíš nás za tak dlouhé časy?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Obrať nás, ó Hospodine, k sobě, a obráceni budeme; obnov dny naše, jakž byly za starodávna.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Nebo zdali všelijak zavržeš nás, a hněvati se budeš na nás velice?