< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Spomeni se, Jahve, što nas je snašlo, pogledaj, vidi sramotu našu!
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Baština naša pade u ruke strancima, domovi naši pripadoše tuđincima.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Siročad smo: oca nemamo, majke su nam kao udovice.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Vodu što pijemo plaćamo novcem, i za drvo valja nam platiti.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Jaram nam je o vratu, gone nas, iscrpljeni smo, ne daju nam predahnuti.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Pružamo ruke k Egiptu i Asiriji da se kruha nasitimo.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Oci naši zgriješiše i više ih nema, a mi nosimo krivice njihove.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Robovi nama zapovijedaju, a nitko da nas izbavi iz ruku njihovih.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Kruh svoj donosimo izlažući život maču u pustinji.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Koža nam gori kao peć užarena, ognjicom od plamena gladi.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Oskvrnuli su žene na Sionu i djevice u gradovima judejskim.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Svojim su rukama vješali knezove, ni lica staračka nisu poštivali.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Mladići su nosili žrvnjeve, djeca padala pod bremenom drva.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Starci su ostavili vrata, mladići više ne sviraju na lirama.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
Radosti nesta iz naših srdaca, naš ples se pretvori u tugovanje.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
Pao je vijenac s naše glave, jao nama što zgriješismo!
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Evo zašto nam srce boluje, evo zašto nam oči se zastiru:
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
zato što Gora sionska opustje i po njoj se šuljaju šakali.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Ali ti, Jahve, ostaješ zauvijek, tvoj je prijesto od koljena do koljena.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Zašto da nas zaboraviš zauvijek, da nas ostaviš za mnoge dane?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Vrati nas k sebi, Jahve, obratit ćemo se, obnovi dane naše kao što nekoć bijahu.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Il' nas hoćeš sasvim zabaciti i na nas se beskrajno srditi?

< Makoki 5 >