< Makoki 4 >

1 Zinariya ta rasa kyanta, hasken zinariya ya dushe! An warwatsar da tsarkakakkun duwatsu masu daraja a kan tituna.
Comment s’est-il obscurci, l’or? Comment a été changée sa couleur éclatante? Comment ont été dispersées les pierres du sanctuaire, à la tête de toutes les places?
2 Dubi samarin Sihiyona masu daraja, waɗanda a dā darajarsu ta isa nauyin zinariya, yanzu ana ɗaukar su a matsayin tukwanen ƙasa, aikin maginin tukwane!
Les fils de Sion illustres et revêtus de l’or le plus pur, comment ont-ils été traités comme des vases d’argile, ouvrages des mains d’un potier?
3 Ko diloli suna ba’ya’yansu nono su sha, amma mutanena sun zama marasa zuciya kamar jiminai a cikin jeji.
Mais les lamies même ont mis à nu leurs mamelles, et ont allaité leurs petits; la fille de mon peuple est cruelle comme une autruche dans le désert.
4 Domin ƙishirwa harshen jarirai ya manne a rufin bakinsu; yaran suna roƙo a ba su burodi, amma ba wanda ya ba su.
La langue de l’enfant à la mamelle s’est attachée à son palais par la soif; les petits enfants ont demandé du pain, et il n’y avait personne qui le leur brisât.
5 Waɗanda a dā sukan ci abinci mai daɗi yanzu su ne masu bara a tituna. Waɗanda a dā suke sa kaya masu kyau yanzu suna kwance a kan tarin toka.
Ceux qui se nourrissaient délicieusement sont morts dans les rues; ceux qui étaient élevés dans la pourpre ont embrassé des immondices.
6 Horon mutanena ya fi na Sodom girma, wadda aka hallaka farat ɗaya ba wani hannu da ya juya ya taimake ta.
ZAU. Et l’iniquité de la fille de mon peuple est devenue plus grande que le péché de Sodome, qui fut renversée en un moment, et les hommes n’y ont pas mis les mains.
7 ’Ya’yan sarakunansu sun fi ƙanƙara haske sun kuma fi madara fari, jikunansu sun fi murjani ja, kyansu kamar shuɗin yakutu.
Ses Nazaréens étaient plus blancs que la neige, plus éclatants que le lait, plus vermeils que l’ivoire antique, plus beaux que le saphir.
8 Amma yanzu sun fi dare duhu; ba a iya gane su a tituna. Fatar jikinsu ta manne da ƙasusuwansu; sun bushe kamar itace.
Leur face est devenue plus noire que des charbons, et ils n’ont pas été reconnus sur les places publiques; leur peau s’est attachée à leurs os, elle est devenue comme du bois.
9 Gara waɗanda aka kashe su da takobi da waɗanda suke mutuwa da yunwa; sun rame domin rashin abinci a gona.
Plus heureux ont été les tués par le glaive que les morts par la faim; car ceux-ci ont dépéri, consumés par la stérilité de la terre.
10 Da hannuwansu mata masu tausayi sun dafa yaransu, suka zama masu abinci sa’ad da aka hallaka mutanena.
Les mains des femmes compatissantes ont fait cuire leurs enfants; ils sont devenus leur nourriture dans la ruine de la fille de mon peuple.
11 Ubangiji ya saki fushinsa; ya zuba zafin fushinsa. Ya hura wuta a Sihiyona ta kuma cinye harsashin gininta.
Le Seigneur a assouvi sa fureur, il a répandu la colère de son indignation; et il a allumé dans Sion un feu qui a dévoré ses fondements.
12 Sarakunan duniya ba su gaskata ba, haka ma mutanen duniya, cewa magabta da maƙiya za su iya shiga ƙofofin Urushalima.
Ils n’ont pas cru, les rois de la terre et tous les habitants de l’univers, que l’ennemi, que l’adversaire entrerait par les portes de Jérusalem:
13 Amma ya faru domin zunuban annabawanta da muguntar firistocinta, waɗanda suka zub da jinin masu adalci a cikinsu.
À cause des péchés de ses prophètes et des iniquités de ses prêtres, qui ont répandu au milieu d’elle le sang des justes.
14 Yanzu suna yawo barkatai a tituna kamar makafi. Sun ƙazantu da jini yadda ba wanda zai kuskura ya taɓa rigunansu.
Ils ont erré en aveugles sur les places publiques, ils se sont souillés par le sang; et comme ils ne pouvaient faire autrement, ils relevèrent leurs robes.
15 “Ku tafi! Ba ku da tsabta!” Haka mutane suke ihu suke ce musu. “Ku tashi daga nan! Ku tashi daga nan! Kada ku taɓa mu!” Sa’ad da suka gudu suna yawo, mutanen waɗansu ƙasashe suka ce, “Ba za su ci gaba da zama a nan ba.”
Retirez-vous, impurs, leur a-t-on crié, retirez-vous, allez-vous-en, ne nous touchez pas; car ils se sont querellés, et tout émus, ils ont dit parmi les nations: Le Seigneur n’habitera plus parmi eux.
16 Ubangiji kansa ya warwatsa su; ya daina duban su. Ba a ba firistoci girma, ba su ba dattawa gata.
La face du Seigneur les a divisés, il ne les regardera plus: ils n’ont pas révéré la face des prêtres, ils n’ont pas eu pitié des vieillards.
17 Idanunmu sun gaji, suna ta dubawa ko taimako zai zo; mu sa ido ko za mu ga ƙasar da za tă iya taimakon mu.
Lorsque nous subsistions encore, nos yeux se sont lassés dans l’attente de notre vain secours, en tenant nos regards attachés sur une nation qui ne pouvait nous sauver.
18 Ana bin sawunmu, ba za mu iya tafiya kan tituna ba. Ƙarshenmu ya kusa, kwanakinmu sun ƙare, gama ƙarshenmu ya zo.
Nos pas ont glissé en parcourant nos places publiques; notre fin s’est approchée; nos jours se sont accomplis, parce qu’est venue notre fin.
19 Masu fafarar mu sun fi gaggafa mai firiya a sararin sama sauri; sun fafare mu a kan duwatsu suna fakon mu a jeji.
Nos persécuteurs ont été plus vite que les aigles du ciel; sur les montagnes ils nous ont poursuivis, dans le désert ils nous ont dressé des pièges.
20 Shafaffe na Ubangiji, numfashin ranmu, ya fāɗi cikin tarkonsu. Muna tunani cewa za mu iya rayuwa cikin sauran mutane a ƙarƙashin inuwarsa.
RÉS. L’esprit de notre bouche, le Christ, le Seigneur a été pris à cause de nos péchés; celui à qui nous avions dit: Sous votre ombre, nous vivrons parmi les nations.
21 Ku yi murna da farin ciki, ya Diyar Edom, ke mai zama a ƙasar Uz. Amma ke ma za a ba ki kwaf; za ki bugu ki zama tsirara.
Réjouis-toi et sois dans l’allégresse, fille d’Edom, qui habites dans la terre de Hus; jusqu’à toi aussi viendra le calice; tu seras enivrée et mise à nu.
22 Ya Diyar Sihiyona, hukuncinki zai ƙare; ba zai sa zaman bautarki yă yi tsayi ba. Amma ya Diyar Edom, zai hukunta zunubinki yă tona tsiraicinki.
THAU. Elle est accomplie, la peine de ton iniquité, fille de Sion; le Seigneur ne t’exilera plus; il a visité ton iniquité, fille d’Edom; il a découvert tes péchés.

< Makoki 4 >