< Makoki 4 >

1 Zinariya ta rasa kyanta, hasken zinariya ya dushe! An warwatsar da tsarkakakkun duwatsu masu daraja a kan tituna.
How is dimmed the gold! changed the most fine gold! Poured out are the stones of the sanctuary, at the top of all the streets.
2 Dubi samarin Sihiyona masu daraja, waɗanda a dā darajarsu ta isa nauyin zinariya, yanzu ana ɗaukar su a matsayin tukwanen ƙasa, aikin maginin tukwane!
The precious sons of Zion, they who were weighed against pure gold, How are they accounted as earthen pitchers, the work of the hands of the potter!
3 Ko diloli suna ba’ya’yansu nono su sha, amma mutanena sun zama marasa zuciya kamar jiminai a cikin jeji.
Even wild dogs, draw out the breast, give suck to their whelps—The daughter of my people, hath become cruel, like the ostriches in the desert.
4 Domin ƙishirwa harshen jarirai ya manne a rufin bakinsu; yaran suna roƙo a ba su burodi, amma ba wanda ya ba su.
The tongue of the suckling, cleaveth to the roof of his mouth for thirst, —Young children, have asked bread, there was none, to break, it to them.
5 Waɗanda a dā sukan ci abinci mai daɗi yanzu su ne masu bara a tituna. Waɗanda a dā suke sa kaya masu kyau yanzu suna kwance a kan tarin toka.
They who used to eat delicacies, are deserted in the streets, —They who used to be carried on crimson, have embraced heaps of refuse.
6 Horon mutanena ya fi na Sodom girma, wadda aka hallaka farat ɗaya ba wani hannu da ya juya ya taimake ta.
And the punishment of the daughter of my people hath grown greater than the punishment of Sodom, —which was overthrown as in a moment, when no hands had been laid violently upon her.
7 ’Ya’yan sarakunansu sun fi ƙanƙara haske sun kuma fi madara fari, jikunansu sun fi murjani ja, kyansu kamar shuɗin yakutu.
Purer were her Nazirites than snow, whiter were they than milk, —more ruddy, in body, than coral, A sapphire, was their beauty of form.
8 Amma yanzu sun fi dare duhu; ba a iya gane su a tituna. Fatar jikinsu ta manne da ƙasusuwansu; sun bushe kamar itace.
Darker than a coal, is their visage, They are not known in the streets—Their skin shrivelleth on their bones, is withered, become like a stick.
9 Gara waɗanda aka kashe su da takobi da waɗanda suke mutuwa da yunwa; sun rame domin rashin abinci a gona.
Better are the slain of the sword, than the slain of the famine, —for, these, pine away, stricken through, wanting the produce of the field.
10 Da hannuwansu mata masu tausayi sun dafa yaransu, suka zama masu abinci sa’ad da aka hallaka mutanena.
The hands of compassionate women, have cooked their own children, —they have served as nourishment to them, in the grievous injury of the daughter of my people.
11 Ubangiji ya saki fushinsa; ya zuba zafin fushinsa. Ya hura wuta a Sihiyona ta kuma cinye harsashin gininta.
Yahweh hath completed his indignation, hath poured out the glow of his anger; and hath kindled a fire in Zion, which hath devoured her foundations.
12 Sarakunan duniya ba su gaskata ba, haka ma mutanen duniya, cewa magabta da maƙiya za su iya shiga ƙofofin Urushalima.
Neither the kings of the earth, nor any of the inhabitants of the world, believed, that an adversary or an enemy, should enter, the gates of Jerusalem!
13 Amma ya faru domin zunuban annabawanta da muguntar firistocinta, waɗanda suka zub da jinin masu adalci a cikinsu.
[It is] for the sins of her prophets, the iniquities of her priests, —who have been pouring out, in her midst, the blood of the righteous!
14 Yanzu suna yawo barkatai a tituna kamar makafi. Sun ƙazantu da jini yadda ba wanda zai kuskura ya taɓa rigunansu.
They have wandered—blind—in the streets, have defiled themselves with blood; so that men may not touch their garments.
15 “Ku tafi! Ba ku da tsabta!” Haka mutane suke ihu suke ce musu. “Ku tashi daga nan! Ku tashi daga nan! Kada ku taɓa mu!” Sa’ad da suka gudu suna yawo, mutanen waɗansu ƙasashe suka ce, “Ba za su ci gaba da zama a nan ba.”
Turn aside! Unclean! have they cried to them, Turn aside! Turn aside! Do not touch! because they have fled, yea, wandered, Men said among the nations, They will not again tarry;
16 Ubangiji kansa ya warwatsa su; ya daina duban su. Ba a ba firistoci girma, ba su ba dattawa gata.
The face of Yahweh, hath scattered them, He will look them out no more: The persons of the priests, they have not respected, To the elders, have they shown no favour.
17 Idanunmu sun gaji, suna ta dubawa ko taimako zai zo; mu sa ido ko za mu ga ƙasar da za tă iya taimakon mu.
Silly shall our eyes fail, for our help that is vain: In our watchtower, have we watched—for a nation that will not save.
18 Ana bin sawunmu, ba za mu iya tafiya kan tituna ba. Ƙarshenmu ya kusa, kwanakinmu sun ƙare, gama ƙarshenmu ya zo.
They have laid snares for our steps, that we cannot walk in our own broadways: Drawn near hath our end, Fulfilled are our days, yea arrived hath our end.
19 Masu fafarar mu sun fi gaggafa mai firiya a sararin sama sauri; sun fafare mu a kan duwatsu suna fakon mu a jeji.
Swifter are our pursuers, than the eagles of the heavens, —Over the mountains, have they come hotly after us, In the wilderness, have they lain in wait for us.
20 Shafaffe na Ubangiji, numfashin ranmu, ya fāɗi cikin tarkonsu. Muna tunani cewa za mu iya rayuwa cikin sauran mutane a ƙarƙashin inuwarsa.
The fragrance of our nostrils, The Anointed of Yahweh, hath been captured in their pits, —of whom we had said—In his shade, shall we live among the nations.
21 Ku yi murna da farin ciki, ya Diyar Edom, ke mai zama a ƙasar Uz. Amma ke ma za a ba ki kwaf; za ki bugu ki zama tsirara.
Rejoice and be glad, O daughter of Edom, thou inhabitress in the and of Uz, —Even unto thee, shall the cup pass along, thou shalt be drunken, and expose thy shame.
22 Ya Diyar Sihiyona, hukuncinki zai ƙare; ba zai sa zaman bautarki yă yi tsayi ba. Amma ya Diyar Edom, zai hukunta zunubinki yă tona tsiraicinki.
Completed is thy punishment, O daughter of Zion, He will no more carry thee away captive—He hath punished thine iniquity, O daughter of Edom, he hath stripped the veil from off thy sins.

< Makoki 4 >