< Makoki 4 >

1 Zinariya ta rasa kyanta, hasken zinariya ya dushe! An warwatsar da tsarkakakkun duwatsu masu daraja a kan tituna.
How is the gold become dim! how is the most fine gold changed! The hallowed stones are cast forth at the head of every street.
2 Dubi samarin Sihiyona masu daraja, waɗanda a dā darajarsu ta isa nauyin zinariya, yanzu ana ɗaukar su a matsayin tukwanen ƙasa, aikin maginin tukwane!
The noble sons of Zion, comparable to fine gold, How are they esteemed as earthen pitchers, the work of the hands of the potter!
3 Ko diloli suna ba’ya’yansu nono su sha, amma mutanena sun zama marasa zuciya kamar jiminai a cikin jeji.
The very jackals reach forth the breast; they suckle their young; But the daughter of my people is become cruel, like the ostriches of the desert.
4 Domin ƙishirwa harshen jarirai ya manne a rufin bakinsu; yaran suna roƙo a ba su burodi, amma ba wanda ya ba su.
The tongue of the sucking child cleaveth to the roof of his mouth for thirst; Young children ask for bread, and no man breaketh it for them.
5 Waɗanda a dā sukan ci abinci mai daɗi yanzu su ne masu bara a tituna. Waɗanda a dā suke sa kaya masu kyau yanzu suna kwance a kan tarin toka.
Those that fed on dainties are desolate in the streets; Those that have been brought up in scarlet embrace the dunghill.
6 Horon mutanena ya fi na Sodom girma, wadda aka hallaka farat ɗaya ba wani hannu da ya juya ya taimake ta.
The punishment of the daughter of my people is greater than the punishment of Sodom, Which was overthrown in a moment, though no hands came against her.
7 ’Ya’yan sarakunansu sun fi ƙanƙara haske sun kuma fi madara fari, jikunansu sun fi murjani ja, kyansu kamar shuɗin yakutu.
Her princes were purer than snow, whiter than milk; More ruddy than coral was their body; Their visage was of sapphire.
8 Amma yanzu sun fi dare duhu; ba a iya gane su a tituna. Fatar jikinsu ta manne da ƙasusuwansu; sun bushe kamar itace.
Now darker than a coal is their countenance; they are not known in the streets. Their skin cleaveth to their bones; it is become dry, like wood.
9 Gara waɗanda aka kashe su da takobi da waɗanda suke mutuwa da yunwa; sun rame domin rashin abinci a gona.
More fortunate are the slain by the sword than the slain by famine; For these pine away, stricken through for want of the fruits of the field.
10 Da hannuwansu mata masu tausayi sun dafa yaransu, suka zama masu abinci sa’ad da aka hallaka mutanena.
The hands of tender-hearted women cooked their own children; They were their food, in the destruction of the daughter of my people.
11 Ubangiji ya saki fushinsa; ya zuba zafin fushinsa. Ya hura wuta a Sihiyona ta kuma cinye harsashin gininta.
Jehovah hath spent upon them his fury; he hath poured out his fierce anger; He hath kindled a fire in Zion, which hath devoured its foundations.
12 Sarakunan duniya ba su gaskata ba, haka ma mutanen duniya, cewa magabta da maƙiya za su iya shiga ƙofofin Urushalima.
The kings of the earth believed not, nor all the inhabitants of the world, That the adversary would enter, and the enemy, within the gates of Jerusalem.
13 Amma ya faru domin zunuban annabawanta da muguntar firistocinta, waɗanda suka zub da jinin masu adalci a cikinsu.
It was on account of the sins of her prophets, and the iniquities of her priests, Who shed in the midst of her the blood of the righteous.
14 Yanzu suna yawo barkatai a tituna kamar makafi. Sun ƙazantu da jini yadda ba wanda zai kuskura ya taɓa rigunansu.
They stumbled like blind men through the streets, polluted with blood, So that men could not touch their garments.
15 “Ku tafi! Ba ku da tsabta!” Haka mutane suke ihu suke ce musu. “Ku tashi daga nan! Ku tashi daga nan! Kada ku taɓa mu!” Sa’ad da suka gudu suna yawo, mutanen waɗansu ƙasashe suka ce, “Ba za su ci gaba da zama a nan ba.”
“Depart! unclean!” men cried to them. “Depart, depart, touch not!” As they fled, they stumbled; men said among the nations, “They shall dwell there no more.”
16 Ubangiji kansa ya warwatsa su; ya daina duban su. Ba a ba firistoci girma, ba su ba dattawa gata.
The anger of Jehovah hath scattered them; he will no more care for them; They paid no regard to the priests, they had no compassion for the elders.
17 Idanunmu sun gaji, suna ta dubawa ko taimako zai zo; mu sa ido ko za mu ga ƙasar da za tă iya taimakon mu.
Still did our eyes fail, looking for help in vain; On our watch-tower did we watch for a nation that could not save us.
18 Ana bin sawunmu, ba za mu iya tafiya kan tituna ba. Ƙarshenmu ya kusa, kwanakinmu sun ƙare, gama ƙarshenmu ya zo.
They laid snares for our steps, so that we could not go in our streets; Our end is near; our days are accomplished, yea, our end is come!
19 Masu fafarar mu sun fi gaggafa mai firiya a sararin sama sauri; sun fafare mu a kan duwatsu suna fakon mu a jeji.
Swifter were our pursuers than the eagles of heaven; They chased us upon the mountains; they laid wait for us in the wilderness.
20 Shafaffe na Ubangiji, numfashin ranmu, ya fāɗi cikin tarkonsu. Muna tunani cewa za mu iya rayuwa cikin sauran mutane a ƙarƙashin inuwarsa.
The breath of our nostrils, the anointed of Jehovah, was taken in their pits, Under whose shadow we said that we should live among the nations.
21 Ku yi murna da farin ciki, ya Diyar Edom, ke mai zama a ƙasar Uz. Amma ke ma za a ba ki kwaf; za ki bugu ki zama tsirara.
Rejoice and be glad, O daughter of Edom, that dwellest in the land of Uz! Yet to thee also shall the cup come! thou shalt be drunken, and shalt expose thy nakedness.
22 Ya Diyar Sihiyona, hukuncinki zai ƙare; ba zai sa zaman bautarki yă yi tsayi ba. Amma ya Diyar Edom, zai hukunta zunubinki yă tona tsiraicinki.
Thy punishment is at an end, O daughter of Zion! no more will he carry thee into captivity; But thine iniquity will he punish, O daughter of Edom! he will uncover thy sins.

< Makoki 4 >