< Makoki 4 >
1 Zinariya ta rasa kyanta, hasken zinariya ya dushe! An warwatsar da tsarkakakkun duwatsu masu daraja a kan tituna.
Aleph. How is the gold become dim, the finest colour is changed, the stones of the sanctuary are scattered in the top of every street?
2 Dubi samarin Sihiyona masu daraja, waɗanda a dā darajarsu ta isa nauyin zinariya, yanzu ana ɗaukar su a matsayin tukwanen ƙasa, aikin maginin tukwane!
Beth. The noble sons of Sion, and they that were clothed with the best gold: how are they esteemed as earthen vessels, the work of the potter’s hands?
3 Ko diloli suna ba’ya’yansu nono su sha, amma mutanena sun zama marasa zuciya kamar jiminai a cikin jeji.
Ghimel. Even the sea monsters have drawn out the breast, they have given suck to their young: the daughter of my people is cruel, like the ostrich in the desert.
4 Domin ƙishirwa harshen jarirai ya manne a rufin bakinsu; yaran suna roƙo a ba su burodi, amma ba wanda ya ba su.
Daleth. The tongue of the sucking child hath stuck to the roof of his mouth for thirst: the little ones have asked for bread, and there was none to break it unto them.
5 Waɗanda a dā sukan ci abinci mai daɗi yanzu su ne masu bara a tituna. Waɗanda a dā suke sa kaya masu kyau yanzu suna kwance a kan tarin toka.
He. They that were fed delicately have died in the streets; they that were brought up in scarlet have embraced the dung.
6 Horon mutanena ya fi na Sodom girma, wadda aka hallaka farat ɗaya ba wani hannu da ya juya ya taimake ta.
Vau. And the iniquity of the daughter of my people is made greater than the sin of Sodom, which was overthrown in a moment, and hands took nothing in her.
7 ’Ya’yan sarakunansu sun fi ƙanƙara haske sun kuma fi madara fari, jikunansu sun fi murjani ja, kyansu kamar shuɗin yakutu.
Zain. Her Nazarites were whiter than snow, purer than milk, more ruddy than the old ivory, fairer than the sapphire.
8 Amma yanzu sun fi dare duhu; ba a iya gane su a tituna. Fatar jikinsu ta manne da ƙasusuwansu; sun bushe kamar itace.
Heth. Their face is now made blacker than coals, and they are not known in the streets: their skin hath stuck to their bones, it is withered, and is become like wood.
9 Gara waɗanda aka kashe su da takobi da waɗanda suke mutuwa da yunwa; sun rame domin rashin abinci a gona.
Teth. It was better with them that were slain by the sword, than with them that died with hunger: for these pined away being consumed for want of the fruits of the earth.
10 Da hannuwansu mata masu tausayi sun dafa yaransu, suka zama masu abinci sa’ad da aka hallaka mutanena.
Jod. The hands of the pitiful women have sodden their own children: they were their meat in the destruction of the daughter of my people.
11 Ubangiji ya saki fushinsa; ya zuba zafin fushinsa. Ya hura wuta a Sihiyona ta kuma cinye harsashin gininta.
Caph. The Lord hath accomplished his wrath, he hath poured out his fierce anger: and he hath kindled a fire in Sion, and it hath devoured the foundations thereof.
12 Sarakunan duniya ba su gaskata ba, haka ma mutanen duniya, cewa magabta da maƙiya za su iya shiga ƙofofin Urushalima.
Lamed. The kings of the earth, and all the inhabitants of the world would not have believed, that the adversary and the enemy should enter in by the gates of Jerusalem.
13 Amma ya faru domin zunuban annabawanta da muguntar firistocinta, waɗanda suka zub da jinin masu adalci a cikinsu.
Mem. For the sins of her prophets, and the iniquities of her priests, that have shed the blood of the just in the midst of her.
14 Yanzu suna yawo barkatai a tituna kamar makafi. Sun ƙazantu da jini yadda ba wanda zai kuskura ya taɓa rigunansu.
Nun. They have wandered as blind men in the streets, they were defiled with blood: and when they could not help walking in it, they held up their skirts.
15 “Ku tafi! Ba ku da tsabta!” Haka mutane suke ihu suke ce musu. “Ku tashi daga nan! Ku tashi daga nan! Kada ku taɓa mu!” Sa’ad da suka gudu suna yawo, mutanen waɗansu ƙasashe suka ce, “Ba za su ci gaba da zama a nan ba.”
Samech. Depart you that are defiled, they cried out to them: Depart, get ye hence, touch not: for they quarrelled, and being removed, they said among the Gentiles: He will no more dwell among them.
16 Ubangiji kansa ya warwatsa su; ya daina duban su. Ba a ba firistoci girma, ba su ba dattawa gata.
Phe. The face of the Lord hath divided them, he will no more regard them: they respected not the persons of the priests, neither had they pity on the ancient.
17 Idanunmu sun gaji, suna ta dubawa ko taimako zai zo; mu sa ido ko za mu ga ƙasar da za tă iya taimakon mu.
Ain. While we were yet standing, our eyes failed, expecting help for us in vain, when we looked attentively towards a nation that was not able to save.
18 Ana bin sawunmu, ba za mu iya tafiya kan tituna ba. Ƙarshenmu ya kusa, kwanakinmu sun ƙare, gama ƙarshenmu ya zo.
Sade. Our steps have slipped in the way of our streets, our end draweth near: our days are fulfilled, for our end is come.
19 Masu fafarar mu sun fi gaggafa mai firiya a sararin sama sauri; sun fafare mu a kan duwatsu suna fakon mu a jeji.
Coph. Our persecutors were swifter than the eagles of the air: they pursued us upon the mountains, they lay in wait for us in the wilderness.
20 Shafaffe na Ubangiji, numfashin ranmu, ya fāɗi cikin tarkonsu. Muna tunani cewa za mu iya rayuwa cikin sauran mutane a ƙarƙashin inuwarsa.
Res. The breath of our mouth, Christ the Lord, is taken in our sins: to whom we said: Under thy shadow we shall live among the Gentiles.
21 Ku yi murna da farin ciki, ya Diyar Edom, ke mai zama a ƙasar Uz. Amma ke ma za a ba ki kwaf; za ki bugu ki zama tsirara.
Sin. Rejoice, and be glad, O daughter of Edom, that dwellest in the land of Hus: to thee also shall the cup come, thou shalt be made drunk, and naked.
22 Ya Diyar Sihiyona, hukuncinki zai ƙare; ba zai sa zaman bautarki yă yi tsayi ba. Amma ya Diyar Edom, zai hukunta zunubinki yă tona tsiraicinki.
Thau. Thy iniquity is accomplished, O daughter of Sion, he will no more carry thee away into captivity: he visited thy iniquity, O daughter of Edom, he hath discovered thy sins. The Prayer of Jeremias the Prophet.