< Makoki 3 >
1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Eu sou o homem que viu a aflição pela vara de seu furor.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Guiou-me e levou-me a trevas, e não à luz.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Com certeza se virou contra mim, revirou sua mão o dia todo.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Fez envelhecer minha carne e minha pele, quebrou meus ossos.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Edificou contra mim, e cercou [-me] de fel e de trabalho.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
Fez-me habitar em lugares escuros, como os que já morrera há muito tempo.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Cercou-me por todos lados, e não posso sair; tornou pesados os meus grilhões.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Até quando clamo e dou vozes, fechou [os ouvidos] à minha oração.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
Cercou meus caminhos com pedras lavradas, retorceu as minhas veredas.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Foi para mim como um urso que espia, como um leão escondido.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Desviou meus caminhos, e fez-me em pedaços; deixou-me desolado.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
Armou seu arco, e me pôs como alvo para a flecha.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
Fez entrar em meus rins as flechas de sua aljava.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
Servi de escárnio a todo o meu povo, de canção ridícula deles o dia todo.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Fartou-me de amarguras, embebedou-me de absinto.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
Quebrou os meus dentes com cascalho, cobriu-me de cinzas.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
E afastou minha alma da paz, fez-me esquecer da boa vida.
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
Então eu disse: Pereceram minha força e minha esperança no SENHOR.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Lembra-te da minha aflição e do meu sofrimento, do absinto e do fel.
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Minha alma se lembra e se abate em mim.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Disto me recordarei na minha mente, por isso terei esperança:
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
É pelas bondades do SENHOR que não somos consumidos, porque suas misericórdias não têm fim.
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
Elas são novas a cada manhã; grande é a tua fidelidade.
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
O SENHOR é minha porção, diz a minha alma; portanto nele esperarei.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Bom é o SENHOR para os que nele esperam, para a alma que o busca.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
É bom esperar e tranquilo aguardar a salvação do SENHOR.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
É bom ao homem levar o jugo em sua juventude.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Sente-se só, e fique quieto; pois ele o pôs sobre si.
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Ponha sua boca no pó; talvez haja esperança.
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Dê a face ao que o ferir; farte-se de insultos.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Pois o Senhor não rejeitará para sempre:
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
Mesmo que cause aflição, ele também se compadecerá segundo a grandeza de suas misericórdias.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Pois não é sua vontade afligir nem entristecer os filhos dos homens.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
Esmagar debaixo de seus pés a todos os prisioneiros da terra,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
Perverter o direito do homem diante da presença do Altíssimo,
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
Prejudicar ao homem em sua causa: o Senhor não aprova ) [tais coisas].
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Quem é que pode fazer suceder [algo] que diz, se o Senhor não tiver mandado?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
Por acaso da boca do Altíssimo não sai tanto a maldição como a bênção?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Por que o homem vivente se queixa da punição de seus próprios pecados?
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Examinemos nossos caminhos, investiguemos, e nos voltemos ao SENHOR.
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Levantemos nossos corações e as mãos a Deus nos céus,
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
[Dizendo: ] Nós transgredimos e fomos rebeldes; tu não perdoaste.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Cobriste-te de ira, e nos perseguiste; mataste sem teres compaixão.
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Cobriste-te de nuvens, para que [nossa] oração não passasse.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Tu nos tornaste como escória e rejeito no meio dos povos.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Todos os nossos inimigos abriram sua boca contra nós.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Medo e cova vieram sobre nós, devastação e destruição.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Rios de águas correm de meus olhos, por causa da destruição da filha de meu povo.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Meus olhos destilam, e não cessam; não haverá descanso,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
Até que o SENHOR preste atenção, e veja desde os céus.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Meus olhos afligem minha alma, por causa de todas as filhas de minha cidade.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Sem motivo meus inimigos me caçam como a um passarinho.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
Tentaram tirar minha vida na masmorra, e lançaram pedras sobre mim.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
As águas inundaram sobre minha cabeça; eu disse: É o meu fim.
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
Invoquei o teu nome, SENHOR, desde a cova profunda.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Ouviste minha voz: não escondas o teu ouvido ao meu suspiro, ao meu clamor.
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Tu te achegaste no dia em que te invoquei; disseste: Não temas.
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Defendeste, Senhor, as causas de minha alma; redimiste minha vida.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Viste, SENHOR, a maldade que me fizeram; julga minha causa.
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Viste toda a vingança deles, todos os seus pensamentos contra mim.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Ouvido os seus insultos, ó SENHOR, todos os seus pensamentos contra mim;
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
As coisas ditas pelos que se levantam contra mim, e seu planos contra mim o dia todo.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Olha para tudo quanto eles fazem; com canções zombam de mim.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Retribui-lhes, SENHOR, conforme a obra de suas mãos.
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Dá-lhes angústia de coração, tua maldição a eles.
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Persegue-os com ira, e destrua-os de debaixo dos céus do SENHOR.