< Makoki 3 >

1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Ich bin der Mann, der tief gebeugt worden ist durch die Rute seines Zorns.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Mich hat er verjagt und in die Finsternis geführt und nicht ans Licht.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Nur gegen mich kehrt er immer wieder den ganzen Tag seine Hand.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Er hat mein Fleisch und meine Haut verschlungen und meine Knochen zermalmt.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Er hat rings um mich her Gift und Drangsal aufgebaut.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
In dunkeln Höhlen läßt er mich wohnen wie längst Verstorbene.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Er hat mich eingemauert, daß ich nicht herauskommen kann; mit ehernen Ketten hat er mich beschwert.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Ob ich auch schreie und rufe, verstopft er doch die Ohren vor meinem Gebet.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
Quadersteine legt er mir in den Weg, krümmt meine Pfade.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Er lauert mir auf wie ein Bär, wie ein Löwe im Dickicht.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Er hat mich auf Abwege gebracht, ist über mich hergefallen und hat mich arg zugerichtet.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
Er hat seinen Bogen gespannt und mich dem Pfeile zum Ziel gesetzt.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
Er hat mir seines Köchers Söhne in die Nieren gejagt.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
Ich bin allem Volk zum Gelächter geworden, ihr Liedlein den ganzen Tag.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Er hat mich mit Bitterkeit gesättigt, mit Wermut getränkt.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
Er ließ meine Zähne sich an Kies zerbeißen, er hat mich mit Asche bedeckt.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
Und du hast meine Seele aus dem Frieden verstoßen, daß ich des Glückes vergaß.
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
Und ich sprach: Meine Lebenskraft ist dahin, meine Hoffnung auf den HERRN.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Sei eingedenk meines Elends, meiner Verfolgung, des Wermuts und des Gifts!
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Beständig denkt meine Seele daran und ist tief gebeugt!
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Dieses aber will ich meinem Herzen vorhalten, darum will ich Hoffnung fassen:
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
Gnadenbeweise des HERRN sind's, daß wir nicht gänzlich aufgerieben wurden, denn seine Barmherzigkeit ist nicht zu Ende;
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
sie ist alle Morgen neu, und deine Treue ist groß!
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
Der HERR ist mein Teil, spricht meine Seele; darum will ich auf ihn hoffen.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Der HERR ist gütig gegen die, welche auf ihn hoffen, gegen die Seele, die nach ihm fragt.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Gut ist's, schweigend zu warten auf das Heil des HERRN.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Es ist einem Manne gut, in seiner Jugend das Joch zu tragen.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Er sitze einsam und schweige, wenn man ihm eines auferlegt!
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Er stecke seinen Mund in den Staub; vielleicht ist noch Hoffnung vorhanden!
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Schlägt ihn jemand, so biete er ihm den Backen dar und lasse sich mit Schmach sättigen!
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Denn der Herr wird nicht ewig verstoßen;
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
sondern wenn er betrübt hat, so erbarmt er sich auch nach der Größe seiner Gnade.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Denn nicht aus Lust plagt und betrübt ER die Menschenkinder.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
Wenn alle Gefangenen eines Landes mit Füßen getreten,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
wenn das Recht eines Mannes vor dem Angesicht des Höchsten gebeugt,
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
die Rechtssache eines Menschen verdreht wird, sollte der Herr es nicht beachten?
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Wer hat je etwas gesagt und es ist geschehen, ohne daß der Herr es befahl?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
Geht nicht aus dem Munde des Höchsten das Böse und das Gute hervor?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Was beklagt sich der Mensch? Es hätte sich wahrlich jeder über seine Sünde zu beklagen!
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Lasset uns unsere Wege erforschen und durchsuchen und zum HERRN zurückkehren!
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Lasset uns unsere Herzen samt den Händen zu Gott im Himmel erheben!
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
Wir sind abtrünnig und widerspenstig gewesen; das hast du nicht vergeben;
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
du hast dich im Zorn verborgen und uns verfolgt; du hast uns ohne Gnade erwürgt;
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
du hast dich in eine Wolke gehüllt, daß kein Gebet hindurchdrang;
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
du hast uns zu Kot und Abscheu gemacht unter den Völkern!
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Alle unsere Feinde haben ihr Maul gegen uns aufgesperrt.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Grauen und Grube wurden uns beschieden, Verwüstung und Untergang.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Es rinnen Wasserbäche aus meinen Augen wegen des Untergangs der Tochter meines Volkes.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Mein Auge tränt unaufhörlich; denn da ist keine Ruhe,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
bis der HERR vom Himmel herabschauen und dareinsehen wird.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Was ich sehen muß, tut meiner Seele weh ob aller Töchter meiner Stadt.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Die mich ohne Ursache hassen, stellten mir heftig nach wie einem Vogel;
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
sie wollten mich in der Grube ums Leben bringen und warfen Steine auf mich.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Die Wasser gingen über mein Haupt; ich sagte: Ich bin verloren!
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
Aber ich rief, HERR, deinen Namen an, tief unten aus der Grube.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Du hörtest meine Stimme: «Verschließe dein Ohr nicht vor meinem Seufzen, vor meinem Hilferuf!»
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Du nahtest dich mir des Tages, als ich dich anrief, du sprachest: Fürchte dich nicht!
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Du führtest, o Herr, die Sache meiner Seele, du rettetest mir das Leben!
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Du hast, o HERR, meine Unterdrückung gesehen; schaffe du mir Recht!
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Du hast all ihre Rachgier gesehen, alle ihre Anschläge wider mich;
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
du hast, o HERR, ihr Schmähen gehört, alle ihre Pläne gegen mich,
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
die Reden meiner Widersacher und ihr beständiges Murmeln über mich.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Siehe doch: ob sie niedersitzen oder aufstehen, so bin ich ihr Spottlied.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Vergilt ihnen, o HERR, nach dem Werk ihrer Hände!
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Gib ihnen Verstockung ins Herz, dein Fluch komme über sie!
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Verfolge sie in deinem Zorn und vertilge sie unter dem Himmel des HERRN hinweg!

< Makoki 3 >