< Makoki 3 >
1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Ich bin der Mann, der Elend sah unter der Rute seines Grimms.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Mich hat er getrieben und geführt in Finsternis und tiefes Dunkel.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Ja, gegen mich kehrt er immer auf neue den ganzen Tag seine Hand.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Aufgerieben hat er mein Fleisch und meine Haut, meine Gebeine zerbrochen,
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
rings um mich aufgebaut Gift und Drangsal,
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
mich in tiefe Finsternis versetzt wie in der Urzeit Verstorbene.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Er hat mich ummauert ohne Ausweg, meine Ketten beschwert;
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
ob ich auch schreie und rufe, er hemmt mein Gebet,
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
vermauerte meine Wege mit Quadern, verstörte meine Pfade.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Ein lauernder Bär war er mir, ein Löwe im Hinterhalt.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Er hat meine Wege in die Irre geführt und mich zerrissen, mich verödet gemacht,
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
hat seinen Bogen gespannt und mich aufgestellt als Ziel für den Pfeil,
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
in meine Nieren gesandt seines Köchers Söhne.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
Ich ward zum Gelächter für alle Völker, ihr Spottlied den ganzen Tag.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Er sättigte mich mit Bitternissen, berauschte mich mit Wermut
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
und ließ meine Zähne Kiesel zermalmen, mich in Asche mich wälzen.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
Du raubtest meiner Seele den Frieden, ich vergaß des Glücks
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
und sprach: dahin ist meine Lebenskraft, mein Vertrauen auf Jahwe.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Gedenke meines Elends und meiner Irrsal, des Wermuts und des Gifts!
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Es gedenkt, es gedenkt und ist gebeugt in mir meine Seele.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Dies will ich zu Herzen nehmen, darum will ich hoffen:
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
Jahwes Gnaden sind ja noch nicht aus, sein Erbarmen ja nicht zu Ende;
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
jeden Morgen ist es neu, groß ist deine Treue!
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
Mein Teil ist Jahwe, spricht meine Seele, darum will ich auf ihn hoffen.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Gütig ist Jahwe gegen die, so auf ihn harren, gegen die Seele, die ihn sucht.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Gut ist's, schweigend zu harren auf die Hilfe Jahwes.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Gut ist's dem Manne, zu tragen das Joch in seiner Jugend.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Er sitze einsam und schweige, weil er's ihm auferlegt.
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Er berühre mit seinem Munde den Staub, vielleicht ist noch Hoffnung;
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
biete dem, der ihn schlägt, die Wange, werde mich Schmach gesättigt.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Denn nicht auf ewig verstößt der Herr.
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
sondern, wenn er betrübt hat, so erbarmt er sich wieder nach der Fülle seiner Gnade.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Denn er plagt nicht aus Lust und betrübt die Menschenkinder.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
Daß man unter die Füße tritt alle Gefangenen des Landes,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
das Recht eines Mannes beugt vor dem Antlitz des Höchsten,
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
eines Menschen Streitsache verdreht, - sollte das der Herr nicht sehn?
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Wer ist, der da sprach, und es geschah, ohne daß der Herr es geboten?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
Geht nicht aus dem Munde des Höchsten hervor das Böse und das Gute?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Was seufzt der Mensch, so lang er lebt? Ein jeder seufze über seine Sünden!
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Laßt uns unsern Wandel prüfen und erforschen und zu Jahwe uns bekehren!
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Laßt uns Herz und Hände erheben zu Gott im Himmel!
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
Wir haben gesündigt und sind ungehorsam gewesen, du hast nicht vergeben,
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
hast dich verhüllt in Zorn und uns verfolgt, gemordet ohne Erbarmen,
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
hast dich in Gewölk verhüllt, daß kein Gebet hindurchdrang.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Zu Kehricht und Abscheu machtest du uns inmitten der Völker.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Ihren Mund rissen auf über uns alle unsere Feinde.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Grauen und Grube ward uns zu teil, Verwüstung und Verderben.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Ströme Wassers thränt mein Auge über das Verderben der Tochter meines Volks.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Ruhelos fließt mein Auge ohne Aufhören,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
bis daß herniederschaue und darein sehe Jahwe vom Himmel.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Meine Thräne zehrt an meiner Seele um alle Töchter meiner Stadt.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Mich jagten, jagten wie einen Vogel die, so mir grundlos feind sind,
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
machten in der Grube mein Leben verstummen und warfen Steine auf mich.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Wasser strömte über mein Haupt; ich dachte: ich bin verloren!
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
Ich rief deinen Namen, Jahwe, aus tief unterster Grube.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Du hörtest mein Rufen: “Verschließe dein Ohr nicht; komm mich zu erquicken, mir zu helfen!”
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Du warst nahe, als ich dich rief, sprachst: “Sei getrost!”
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Du führtest, o Herr, meine Sache, erlöstest mein Leben.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Du hast, o Jahwe, meine Unterdrückung gesehn, hilf mir zu meinem Recht!
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Du hast all' ihre Rachgier gesehn, all' ihre Pläne wider mich,
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
hast ihr Schmähen gehört, o Jahwe, all' ihre Pläne wider mich,
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
die Reden meiner Widersacher und ihr stetes Trachten wider mich.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Schau, ob sie sitzen oder aufstehen, ich bin ihr Spottlied!
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Du wirst ihnen lohnen, Jahwe, nach ihrer Hände Werk,
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
wirst ihr Herz verstocken - dein Fluch über sie!
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Du wirst sie im Zorn verfolgen und vertilgen unter Jahwes Himmel weg!