< Makoki 3 >

1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Ich bin der Mann, der Elend hat erfahren durch seines Grimmes Rute.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Mich drängte er und führte mich in Finsternis und tiefes Dunkel.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
An mir erprobt er immer wieder seine Macht den ganzen Tag.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Er rieb mir auf mein Fleisch und meine Haut, zerbrach mir mein Gebein.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Und eingeschritten ist er gegen mich mit Gift und Aufhängen,
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
versetzte mich in Finsternis wie ewig Tote.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Er mauerte mich ein, ließ keinen Ausweg offen, beschwerte mich mit Ketten.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Ob ich auch schreie, rufe, er weist mein Beten ab,
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
versperrt mit Pfählen meine Wege, verstört mir meine Pfade.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Er ist mir wie ein Bär, der lauert, ein Löwe in dem Hinterhalt.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Er kreist um meine Wege, umschließt mich, macht mich einsam,
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
dann spannt er seinen Bogen und stellt als Ziel mich auf für seine Pfeile.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
Er schießt mir in die Nieren des Köchers Söhne.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
Ich wurde meinem ganzen Volke zum Gespött, ihr Spottlied für den ganzen Tag.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Mit Bitternissen machte er mich satt, berauschte mich mit Wermut,
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
zermalmen ließ er meine Zähne Kiesel und wälzte mich im Staube.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
Des Glücks beraubt ward meine Seele, daß ich des Heiles ganz vergaß
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
und sprach: "Dahin ist meine Lebenskraft und meine Hoffnung auf den Herrn."
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Ja, der Gedanke an mein Elend, meine Irrsale, ist Wermut mir und Gift.
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Und doch denkt meine Seele dran und sinnt in mir.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Und ich bedachte dies und schöpfte daraus meine Hoffnung.
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
Des Herren Huld ist nicht zu Ende und sein Erbarmen nicht erschöpft.
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
Neu ist's an jedem Morgen; ja: "Groß ist Deine Treue;
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
mein Anteil ist der Herr", spricht meine Seele; "drum hoffe ich auf ihn."
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Der Herr ist denen gütig, die seiner harren, und einer Seele, die ihn sucht.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Drum ist es gut, schweigend des Herren Hilfe zu erwarten.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Gar heilsam ist es für den Mann, das Joch in seiner Jugend schon zu tragen.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Er sitze einsam da und schweige, weil er's ihm auferlegt!
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Mit seinem Mund berühre er den Staub! Vielleicht gibt's dann noch Hoffnung.
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Er biete seine Wange jenem dar, der nach ihm schlägt, und lasse sich mit Schmach ersättigen!
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Denn nicht auf ewig will der Herr verstoßen.
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
Und fügt er auch Betrübnis zu, erbarmt er sich auch wieder seiner Gnadenfülle nach.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Denn nicht aus Lust erniedrigt er und beugt die Menschenkinder,
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
damit man mit den Füßen all die Gefangenen des Landes trete,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
daß man das Recht der Leute beuge, das sie beim Allerhöchsten haben.
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
Daß jemandem sein Recht genommen wird, das kann der Herr nicht billigen.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Wer ist's, der sprach, und es geschah, und nicht befohlen hätte es der Herr?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
Ja, kommt nicht aus des Höchsten Mund das Schlimme wie das Gute?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Was klagt ein Mensch im Leben, ein Mann ob seiner Sündenstrafe?
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Laßt uns doch unsern Wandel prüfen und erforschen und uns zum Herrn bekehren!
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Laßt uns die Herzen lieber als die Hände zu Gott im Himmel heben:
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
"Gesündigt haben wir in Widerspenstigkeit; Du hast uns nicht vergeben.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Du hast mit Zorn uns ganz bedeckt, verfolgt, gemordet mitleidlos.
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Du hast Dich in Gewölk gehüllt, daß kein Gebet hindurch mehr dringe.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Zu Kehricht und zum Auswurf hast Du uns gemacht inmitten jener Völker.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Weit rissen über uns den Mund all unsre Feinde auf.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Zu Angst und Furcht ward uns Verwüstung und Verderben."
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Mein Auge weinte Wasserströme ob der Vernichtung, die getroffen meines Volkes Tochter.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Und ohne Ruhe fließt mein Auge und ohne Rasten,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
bis daß herniederschaue und es sehe der Herr vom Himmel.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Mein Auge klagt ohn Ende ob all den Töchtern meiner Stadt.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Mich jagten hin und her wie einen Vogel, die mir so grundlos Feinde waren.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
Mein Leben wollten sie vernichten in der Grube; mit Steinen warfen sie auf mich.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Dann strömte übers Haupt mir Wasser; ich sprach: "Ich bin verloren."
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
Da rief ich Deinen Namen, Herr, aus tiefster Grube an.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Du hörtest meine Stimme: "Ach, verschließe meinem Rufen und meinem Seufzen nicht Dein Ohr!"
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Du nahtest, als ich Dich gerufen; Du sprachst: "Sei nur getrost!"
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Du führtest meine Sache, Herr; Du wahrtest mir das Leben.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Nun siehst Du, Herr: Bedrückt bin ich. Verhilf zu meinem Rechte mir!
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
All ihre Rachgier schauest Du, all ihre Pläne gegen mich,
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Du hörst ihr Schmähen, Herr, und all ihr Planen gegen mich,
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
die Reden meiner Widersacher, ihr stetes Trachten gegen mich.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Ihr Sitzen und ihr Aufstehn schau Dir an! Zum Spottlied bin ich ihnen.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Du lohnest ihnen, Herr, nach ihrer Hände Werk.
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Verblendung gibst Du ihrem Herzen, gibst ihnen Deinen Fluch.
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Im Zorn verfolgst Du sie und tilgst sie unterm Himmel, Herr.

< Makoki 3 >