< Makoki 3 >
1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Je suis un homme voyant ma misère sous la verge de son indignation.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Il m’a conduit et amené dans les ténèbres et non à la lumière.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
C’est seulement contre moi qu’il tourne et retourne sa main durant tout le jour.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Il a fait vieillir ma peau et ma chair, il a brisé mes os.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Il a bâti autour de moi, et il m’a environné de fiel et de peine.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
Il m’a mis dans des lieux ténébreux comme les morts éternels.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Il a bâti autour de moi, afin que je ne sorte pas; il a appesanti mes fers aux pieds.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Mais lors même que je crierais et que je prierais, il a repoussé ma prière.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
Il a fermé mes voies avec des pierres de taille, il a détruit mes sentiers.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Il est devenu pour moi un ours en embuscade, un lion dans des lieux cachés.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Il a détruit mes sentiers et il m’a brisé, il m’a mis dans la désolation.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
Il a tendu son arc, il m’a fait comme le but de ses flèches.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
Il a lancé dans mes reins les filles de son carquois.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
Je suis devenu la raillerie de tout mon peuple, leur chanson durant tout le jour.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Il m’a rempli d’amertume, il m’a enivré d’absinthe.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
Et il a brisé toutes mes dents, il m’a nourri de cendre.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
Et mon âme a été éloignée de la paix, et j’ai oublié le bonheur.
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
Et j’ai dit: Elle a péri, ma fin, et ce que j’espérais du Seigneur.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Souvenez-vous de ma pauvreté, et de l’excès commis contre moi, de l’absinthe et du fiel.
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
J’en conserverai toujours la mémoire, et mon âme séchera en moi de douleur.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Je repasserai ces choses dans mon cœur, c’est pourquoi j’espérerai.
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
C’est grâce aux miséricordes du Seigneur que nous n’avons pas été consumés; c’est parce que ses bontés n’ont pas fait défaut.
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
Elles se renouvellent au point du jour; votre fidélité est grande.
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
Mon partage est le Seigneur, a dit mon âme; à cause de cela je l’attendrai.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Le Seigneur est bon à ceux qui espèrent en lui, à l’âme qui le recherche.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Il est bon d’attendre en silence le salut de Dieu.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Il est bon à l’homme de porter un joug dès sa jeunesse.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Il s’assiéra solitaire, et il se taira, parce qu’il a mis ce joug sur lui.
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Il mettra sa bouche dans la poussière, pourvoir si par hasard il y a espérance.
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Il tendra la joue à celui qui le frappera, il sera rassasié d’opprobres.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Parce que le Seigneur ne rejettera pas toujours;
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
Parce que s’il a rejeté, il aura aussi pitié selon la multitude de ses miséricordes.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Car il n’a pas humilié d’après son cœur, il n’a pas rejeté les fils des hommes,
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
Afin de fouler sous ses pieds tous les captifs de la terre,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
Afin de faire incliner le droit de l’homme devant la face du Très-Haut.
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
Perdre un homme dans son jugement, le Seigneur ne le sait pas.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Qui est celui qui a dit qu’une chose se fît, le Seigneur ne l’ayant pas commandé?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
De la bouche du Très-Haut, les maux et les biens ne sortiront-ils pas?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Pourquoi a murmuré l’homme vivant, l’homme, de la punition de ses péchés?
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Scrutons nos voies, interrogeons-les, et retournons au Seigneur.
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Elevons nos cœurs avec nos mains vers le Seigneur qui est dans les cieux.
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
Nous, nous avons iniquement agi, et au courroux nous vous avons provoqué, c’est pour cela que vous êtes inexorable.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Vous vous êtes enveloppé dans votre fureur, et vous nous avez frappés; vous avez tué et vous n’avez pas épargné.
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Vous avez mis une nuée devant vous, afin que la prière ne passe pas.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Comme une plante arrachée et rejetée, vous m’avez mis au milieu des peuples.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Tous nos ennemis ont ouvert la bouche contre nous.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
La prophétie nous est devenue effroi, lacs et ruine.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Mon œil a fait couler des courants d’eaux sur la ruine de la fille de mon peuple.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Mon œil s’est affligé, et ne s’est pas tu, de ce qu’il n’y avait point de repos,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
Jusqu’à ce que le Seigneur regardât et vît des cieux.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Mon œil a tourmenté mon âme à cause de toutes les filles de ma ville.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Ils m’ont pris à la chasse comme un oiseau, mes ennemis, sans sujet.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
Ma vie est tombée dans la fosse, et ils ont posé une pierre sur moi.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Des eaux se sont débordées sur ma tête; j’ai dit: Je suis perdu.
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
J’ai invoqué votre nom, Seigneur, du lac le plus profond.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Vous avez entendu ma voix; ne détournez pas votre oreille de mes sanglots et de mes cris.
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Vous vous êtes approché de moi un jour, quand je vous ai invoqué; vous avez dit: Ne crains pas.
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Vous avez jugé, Seigneur, la cause de mon âme, rédempteur de ma vie.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Vous avez vu. Seigneur, leur iniquité contre moi; jugez leur jugement.
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Vous avez vu toute leur fureur, toutes leurs pensées contre moi.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Vous avez entendu leurs outrages, Seigneur, toutes leurs pensées contre moi;
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
Les lèvres de ceux qui s’élèvent contre moi, et leurs projets contre moi tout le jour.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Quand ils sont assis, et quand ils se lèvent, voyez, je suis l’objet de leurs chansons.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
THAU. Vous leur rendrez la pareille, Seigneur, selon les œuvres de leurs mains.
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
THAU. Vous leur mettrez comme un bouclier sur le cœur, la peine dont vous les accablerez.
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
THAU. Vous les poursuivrez dans votre fureur, et vous les briserez sous le ciel. Seigneur.