< Makoki 3 >

1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Je suis l’homme qui a vu la misère Sous la verge de sa fureur.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Il m’a conduit, mené dans les ténèbres, Et non dans la lumière.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Contre moi il tourne et retourne sa main Tout le jour.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Il a fait dépérir ma chair et ma peau, Il a brisé mes os.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Il a bâti autour de moi, Il m’a environné de poison et de douleur.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
Il me fait habiter dans les ténèbres, Comme ceux qui sont morts dès longtemps.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Il m’a entouré d’un mur, pour que je ne sorte pas; Il m’a donné de pesantes chaînes.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
J’ai beau crier et implorer du secours, Il ne laisse pas accès à ma prière.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
Il a fermé mon chemin avec des pierres de taille, Il a détruit mes sentiers.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Il a été pour moi un ours en embuscade, Un lion dans un lieu caché.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Il a détourné mes voies, il m’a déchiré, Il m’a jeté dans la désolation.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
Il a tendu son arc, et il m’a placé Comme un but pour sa flèche.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
Il a fait entrer dans mes reins Les traits de son carquois.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
Je suis pour tout mon peuple un objet de raillerie, Chaque jour l’objet de leurs chansons.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Il m’a rassasié d’amertume, Il m’a enivré d’absinthe.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
Il a brisé mes dents avec des cailloux, Il m’a couvert de cendre.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
Tu m’as enlevé la paix; Je ne connais plus le bonheur.
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
Et j’ai dit: Ma force est perdue, Je n’ai plus d’espérance en l’Éternel!
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Quand je pense à ma détresse et à ma misère, A l’absinthe et au poison;
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Quand mon âme s’en souvient, Elle est abattue au-dedans de moi.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Voici ce que je veux repasser en mon cœur, Ce qui me donnera de l’espérance.
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
Les bontés de l’Éternel ne sont pas épuisées, Ses compassions ne sont pas à leur terme;
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
Elles se renouvellent chaque matin. Oh! Que ta fidélité est grande!
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
L’Éternel est mon partage, dit mon âme; C’est pourquoi je veux espérer en lui.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
L’Éternel a de la bonté pour qui espère en lui, Pour l’âme qui le cherche.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Il est bon d’attendre en silence Le secours de l’Éternel.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Il est bon pour l’homme De porter le joug dans sa jeunesse.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Il se tiendra solitaire et silencieux, Parce que l’Éternel le lui impose;
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Il mettra sa bouche dans la poussière, Sans perdre toute espérance;
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Il présentera la joue à celui qui le frappe, Il se rassasiera d’opprobres.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Car le Seigneur Ne rejette pas à toujours.
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
Mais, lorsqu’il afflige, Il a compassion selon sa grande miséricorde;
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Car ce n’est pas volontiers qu’il humilie Et qu’il afflige les enfants des hommes.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
Quand on foule aux pieds Tous les captifs du pays,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
Quand on viole la justice humaine A la face du Très-Haut,
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
Quand on fait tort à autrui dans sa cause, Le Seigneur ne le voit-il pas?
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Qui dira qu’une chose arrive, Sans que le Seigneur l’ait ordonnée?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
N’est-ce pas de la volonté du Très-Haut que viennent Les maux et les biens?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Pourquoi l’homme vivant se plaindrait-il? Que chacun se plaigne de ses propres péchés.
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Recherchons nos voies et sondons, Et retournons à l’Éternel;
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Élevons nos cœurs et nos mains Vers Dieu qui est au ciel:
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
Nous avons péché, nous avons été rebelles! Tu n’as point pardonné!
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Tu t’es caché dans ta colère, et tu nous as poursuivis; Tu as tué sans miséricorde;
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Tu t’es enveloppé d’un nuage, Pour fermer accès à la prière.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Tu nous as rendus un objet de mépris et de dédain Au milieu des peuples.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Ils ouvrent la bouche contre nous, Tous ceux qui sont nos ennemis.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Notre partage a été la terreur et la fosse, Le ravage et la ruine.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Des torrents d’eau coulent de mes yeux, A cause de la ruine de la fille de mon peuple.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Mon œil fond en larmes, sans repos, Sans relâche,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
Jusqu’à ce que l’Éternel regarde et voie Du haut des cieux;
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Mon œil me fait souffrir, A cause de toutes les filles de ma ville.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Ils m’ont donné la chasse comme à un oiseau, Ceux qui sont à tort mes ennemis.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
Ils ont voulu anéantir ma vie dans une fosse, Et ils ont jeté des pierres sur moi.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Les eaux ont inondé ma tête; Je disais: Je suis perdu!
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
J’ai invoqué ton nom, ô Éternel, Du fond de la fosse.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Tu as entendu ma voix: Ne ferme pas l’oreille à mes soupirs, à mes cris!
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Au jour où je t’ai invoqué, tu t’es approché, Tu as dit: Ne crains pas!
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Seigneur, tu as défendu la cause de mon âme, Tu as racheté ma vie.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Éternel, tu as vu ce qu’on m’a fait souffrir: Rends-moi justice!
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Tu as vu toutes leurs vengeances, Tous leurs complots contre moi.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Éternel, tu as entendu leurs outrages, Tous leurs complots contre moi,
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
Les discours de mes adversaires, et les projets Qu’ils formaient chaque jour contre moi.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Regarde quand ils sont assis et quand ils se lèvent: Je suis l’objet de leurs chansons.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Tu leur donneras un salaire, ô Éternel, Selon l’œuvre de leurs mains;
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Tu les livreras à l’endurcissement de leur cœur, A ta malédiction contre eux;
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Tu les poursuivras dans ta colère, et tu les extermineras De dessous les cieux, ô Éternel!

< Makoki 3 >