< Makoki 3 >

1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Je suis l’homme qui a connu la misère sous la verge de son courroux.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
C’Est moi qu’il a poussé et fait marcher dans des ténèbres que ne traverse aucune lueur.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Oui, contre moi il revient à la charge et tourne sa main tout le temps.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Il a consumé ma chair et ma peau, brisé mes os.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Il a bâti une clôture autour de moi et m’a enveloppé de venin et de tribulations.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
Il m’a relégué dans des régions ténébreuses comme les morts, endormis pour toujours.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Il m’a entouré d’un mur que je ne puis franchir, chargé de lourdes chaînes.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
En vain je crie et appelle au secours, il ferme tout accès à ma prière.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
Il barre mes routes avec des pierres de taille, il bouleverse mes sentiers.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Il est pour moi un ours aux aguets, un lion en embuscade.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Il a rendu impraticables mes voies et m’a déchiré; il a fait de moi une ruine.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
Il a bandé son arc et m’a dressé comme une cible à ses traits.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
Il fait pénétrer dans mes reins les enfants de son carquois.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
Je suis devenu la risée de tous les peuples, un thème de leurs chansons incessantes.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Il m’a rassasié d’herbes amères, abreuvé d’absinthe.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
Il a broyé mes dents avec du gravier, il m’a roulé dans la cendre.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
Mon âme a dit adieu à la paix, j’ai perdu jusqu’au souvenir du bonheur,
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
et j’ai dit: "C’En est fait de mon avenir et de ce que je pouvais espérer de l’Eternel."
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Rappelle-toi ma misère et mon abandon: je ne connais que poison et absinthe.
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
En évoquant ces souvenirs, mon âme s’affaisse en moi.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Mais voici la pensée qui s’éveille en moi, et c’est pourquoi j’espère.
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
C’Est que les bontés de l’Eternel ne sont pas taries et que sa miséricorde n’est pas épuisée.
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
Elles se renouvellent chaque matin, infinie est ta bienveillance.
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
"L’Eternel est mon lot, dit mon âme, aussi espéré-je en lui."
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
L’Eternel est bon pour ceux qui mettent leur confiance en lui, pour l’âme qui le recherche.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
C’Est une bonne chose d’attendre en silence le secours de l’Eternel;
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
une bonne chose aussi pour l’homme de porter le joug dès sa jeunesse;
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
de s’asseoir solitaire en se résignant silencieusement, lorsque Dieu le lui impose.
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Qu’il incline sa bouche vers la poussière: peut-être est-il quelque espoir.
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Qu’il présente la joue à celui qui le frappe et se rassasie d’humiliation
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
car le Seigneur ne délaisse pas à tout jamais;
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
mais quand il a frappé, il exerce sa pitié selon l’étendue de sa bonté.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Car ce n’est pas de bon cœur qu’il moleste et afflige les fils de l’homme.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
Lorsqu’on foule aux pieds tous les captifs du pays,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
lorsqu’on fait fléchir le droit d’un homme à la face du Très-Haut,
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
lorsqu’on fait tort à un homme dans sa juste cause, le Seigneur ne peut l’approuver.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
A qui donc suffit-il d’ordonner pour qu’une chose soit, si le Seigneur n’en a décidé ainsi?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
N’Est-ce pas de la bouche de l’Eternel qu’émanent les maux et les biens?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Pourquoi donc se plaindrait l’homme sa vie durant, l’homme chargé de péchés?
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Examinons nos voies, scrutons-les et retournons à l’Eternel!
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Elevons nos cœurs avec nos mains vers Dieu qui est au ciel!
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
Nous, nous avons failli et désobéi: toi, tu n’as point pardonné.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Tu t’es enveloppé de colère et tu nous as persécutés; tu as tué sans ménagement.
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Tu t’es entouré de nuages, pour empêcher les prières de passer.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Tu as fait de nous une balayure, un objet de dégoût au milieu des nations.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Tous nos ennemis ont ouvert la bouche contre nous.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Notre partage, ce furent la terreur et le piège, la ruine et le désastre.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Mes yeux se répandent en torrents de larmes à cause de la catastrophe de mon peuple.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Mes yeux se fondent en eau sans s’arrêter, car il n’est point de répit au mal,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
jusqu’à ce que l’Eternel regarde et voie du haut du ciel.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Le spectacle qui s’offre à mes regards accable mon âme à cause de toutes les filles de ma ville.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Ils m’ont pourchassé comme un passereau, ceux qui me haïssent sans motif.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
Ils ont confiné ma vie dans la fosse et jeté des pierres sur moi.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Les eaux ont monté par-dessus ma tête, et j’ai dit: "Je suis perdu!"
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
Mais j’ai invoqué ton nom des profondeurs de la fosse.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Tu as entendu mon appel: "Ne ferme pas ton oreille alors que je supplie pour ma délivrance."
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Tu es venu près de moi le jour où je t’ai invoqué, tu as dit: "Sois sans crainte!"
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Tu as pris en mains les causes qui me touchent, tu sauves ma vie.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Tu as vu, Eternel, le tort qu’on m’a fait: défends mon droit!
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Tu as été témoin de leurs représailles, de tous leurs complots contre moi.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Tu as entendu, Eternel, 'leurs outrages, toutes leurs machinations contre moi.
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
Les lèvres de mes adversaires et leurs pensées sont dirigées contre ma personne.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Regarde leurs faits et gestes: je suis l’objet de leurs chants moqueurs.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Puisses-tu leur rendre la pareille, ô Eternel, les traiter selon l’oeuvre de leurs mains!
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Inflige-leur l’angoisse du cœur: ta malédiction vienne sur eux!
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Poursuis-les de ton courroux et anéantis-les de dessous la voûte de tes cieux.

< Makoki 3 >