< Makoki 3 >
1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Je suis l’homme qui a vu l’affliction, sous la verge de sa fureur.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Il m’a conduit et m’a fait marcher dans les ténèbres et non dans la lumière;
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
contre moi seul il tourne et retourne sa main tout le jour. BETH.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Il a usé ma chair et ma peau, il a brisé mes os;
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Il a bâti contre moi, il m’a environné d’amertume et d’ennui.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
Il m’a fait habiter dans les ténèbres, comme ceux qui sont morts depuis longtemps. GHIMEL.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Il m’a entouré d’un mur pour que je ne puisse sortir, il a rendu lourdes mes chaînes.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Lors même que je crie et que j’implore, il ferme tout accès à ma prière.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
Il a muré mes chemins avec des pierres de taille, il a bouleversé mes sentiers. DALETH.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Il a été pour moi comme un ours aux aguets, comme un lion dans les embuscades;
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
il a détourné mes voies et m’a mis en pièces, il m’a réduit à l’abandon;
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
il a bandé son arc et m’a placé comme but à ses flèches. HÉ.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
Il a fait pénétrer dans mes reins les fils de son carquois;
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
je suis la risée de tout mon peuple, leur chanson tout le jour;
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
il m’a rassasié d’amertume, il m’a abreuvé d’absinthe. VAV.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
Et il a fait broyer du gravier à mes dents, il m’a enfoncé dans la cendre;
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
et mon âme est violemment écartée de la sécurité; j’ai oublié le bonheur;
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
et j’ai dit: « Ma force est perdue, ainsi que mon espérance en Yahweh! » ZAÏN.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Souviens-toi de mon affliction et de ma souffrance, de l’absinthe et de l’amertume!
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Mon âme s’en souvient sans cesse, et elle est abattue en moi.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Voici ce que je me rappellerai en mon cœur, et ce pourquoi j’espérerai: HETH.
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
C’est une grâce de Yahweh que nous ne soyons pas anéantis, car ses miséricordes ne sont pas épuisées!
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
Elles se renouvellent chaque matin; grande est ta fidélité!
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
« Yahweh est mon partage, a dit mon âme; c’est pourquoi j’espérerai en lui. » TETH.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Yahweh est bon pour qui espère en lui, pour l’âme qui le cherche.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Il est bon d’attendre en silence la délivrance de Yahweh.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Il est bon à l’homme de porter le joug dès sa jeunesse. JOD.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Qu’il s’asseye à l’écart, en silence, si Dieu le lui impose!
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Qu’il mette sa bouche dans la poussière: peut-être y a-t-il de l’espérance!
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Qu’il tende la joue à celui qui le frappe; qu’il se rassasie d’opprobre! CAPH.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Car le Seigneur ne rejette pas à toujours;
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
mais, s’il afflige, il a compassion, selon sa grande miséricorde;
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
car ce n’est pas de bon cœur qu’il humilie, et qu’il afflige les enfants des hommes. LAMED.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
Quand on foule aux pieds tous les captifs du pays,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
quand on fait fléchir le droit d’un homme, à la face du Très-Haut,
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
quand on fait tort à quelqu’un dans sa cause, le Seigneur ne le verrait donc pas! MEM.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Qui a parlé, et la chose s’est faite, sans que le Seigneur l’ait commandé?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
N’est-ce pas de la bouche du Très-Haut que procèdent les maux et les biens?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Pourquoi l’homme se plaindrait-il tant qu’il vit? Que chacun se plaigne de ses péchés! NUN.
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Examinons nos voies et scrutons-les, et retournons à Yahweh.
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Élevons nos cœurs, avec nos mains, vers Dieu dans les cieux:
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
« Nous, nous avons péché, nous avons été rebelles; toi, tu n’as pas pardonné. » SAMECH.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
« Tu t’es enveloppé dans ta colère, et tu nous as poursuivis; tu as tué sans épargner;
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Tu t’es couvert d’une nuée, afin que la prière ne passe point;
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
tu as fait de nous des balayures et un rebut, au milieu des peuples. » PHÉ.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Ils ouvrent la bouche contre nous, tous nos ennemis.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
La frayeur et la fosse ont été notre part, ainsi que la dévastation et la ruine.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Mon œil se fond en un ruisseau de larmes, à cause de la ruine de la fille de mon peuple. AÏN.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Mon œil pleure et ne cesse point, parce qu’il n’y a pas de répit,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
jusqu’à ce qu’il regarde et voie, Yahweh, du haut des cieux.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Mon œil fait mal à mon âme, à cause de toutes les filles de ma ville. TSADÉ.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Ils m’ont donné la chasse comme a un passereau, ceux qui me haïssent sans cause.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
Ils ont voulu anéantir ma vie dans la fosse, et ils ont jeté une pierre sur moi.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Les eaux montaient au-dessus de ma tête; je disais: « Je suis perdu! » QOPH.
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
J’ai invoqué ton nom, Yahweh, de la fosse profonde;
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
tu as entendu ma voix: « Ne ferme point ton oreille à mes soupirs, à mes cris! »
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Tu t’es approché, au jour où je t’ai invoqué, et tu as dit: « Ne crains point! » RESCH.
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Seigneur tu as pris en main ma cause, tu m’as sauvé la vie.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Tu as vu, Yahweh, la violence qu’ils me font; fais-moi justice!
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Tu as vu toute leur rancune, tous leurs complots contre moi. SIN.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Tu as entendu leurs outrages, Yahweh, tous leurs complots contre moi,
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
les propos de mes adversaires et ce qu’ils méditent, contre moi tout le jour.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Quand ils s’asseyent ou qu’ils se lèvent, regarde: je suis l’objet de leurs chansons. THAV.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Tu leur rendras, Yahweh, ce qu’ils méritent, selon l’œuvre de leurs mains;
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Tu leur donneras l’aveuglement du cœur; ta malédiction sera pour eux.
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Tu les poursuivras avec colère et tu les extermineras, de dessous les cieux de Yahweh!