< Makoki 3 >

1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
I [am] the man [who] he has seen affliction by [the] rod of fury his.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Me he has driven and he has made walk darkness and not light.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Surely on me he returned he turned hand his all the day.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
He has made to waste away flesh my and skin my he has broken bones my.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
He has built on me and he has surrounded [me] poison and hardship.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
In dark places he has caused to dwell me like dead people of antiquity.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
He has walled up behind me and not I will go out he has made heavy bronze fetter[s] my.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Also if I will cry out and I may cry for help he has shut out prayer my.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
He has walled up ways my with hewn [stone] paths my he has made crooked.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
[is] a bear Lying in wait he to me (a lion *Q(K)*) in hiding places.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Ways my he has caused to deviate and he has torn in pieces me he has made me desolate.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
He has bent (bow his *L(abh)*) and he has set up me like target for arrow.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
He has brought in kidneys my [the] sons of quiver his.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
I have become a laughingstock to all people my taunt song their all the day.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
He has surfeited me with bitter things he has made drink me wormwood.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
And he has broken with gravel teeth my he has made cower me in ash[es].
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
And it has excluded from peace self my I have forgotten good.
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
And I said it has perished endurance my and hope my from Yahweh.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Remember affliction my and homelessness my wormwood and poison.
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Continually it remembers (so it may bow down *Q(K)*) on me self my.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
This I bring back to heart my there-fore I will wait.
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
[the] covenant loyalti of Yahweh for not we have met our end for not they come to an end compassion his.
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
[they are] new To the mornings [is] great faithfulness your.
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
[is] portion My Yahweh it has said self my there-fore I will wait for him.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
[is] good Yahweh (to [those who] wait for him *Q(K)*) to anyone [who] it will seek him.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
[is] good And waiting and silently for [the] salvation of Yahweh.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
[is] good For man that he will bear a yoke in youth his.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Let him sit alone and let him be silent for he has laid [it] on him.
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Let him put in the dust mouth his perhaps there [is] hope.
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Let him give to [the] [one who] strikes him a cheek let him be sated with reproach.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
For not he will reject for ever [the] Lord.
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
That except he has caused grief and he will have compassion according to [the] greatness of (covenant loyalti his. *Q(K)*)
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
For not he has afflicted from heart his and he has grieved ([the] children of *L(abh)*) a man.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
To crush under feet his all [the] prisoners of [the] land.
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
To turn aside [the] justice of a man before [the] presence of [the] Most High.
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
To subvert anyone in case at law his [the] Lord not he has seen.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Who? this has he spoken and it was [the] Lord not he commanded [it].
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
From [the] mouth of [the] Most High not does it goes forth? the troubles and the good.
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Why? will he complain a person living a man on (sins his. *Q(K)*)
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Let us examine ways our and let us examine and let us return to Yahweh.
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Let us lift up heart our to palms to God in the heavens.
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
We we have transgressed and we have rebelled you not you have forgiven.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
You have covered yourself with anger and you have pursued us you have killed not you have spared.
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
You have covered with cloud yourself from passing through prayer of.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Scouring and refuse you have made us in [the] midst of the peoples.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
They have opened on us mouth their all enemies our.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Terror and a pit it has happened to us devastation and brokenness.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Streams of water it goes down eye my on [the] brokenness of [the] daughter of people my.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Eye my it has poured itself and not it will cease from not stop.
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
Until he will look down and he will see Yahweh from heaven.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Eye my it has dealt severely to self my from all [the] daughters of city my.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Certainly they hunted me like bird enemies my without cause.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
They destroyed in the pit life my and they threw down a stone on me.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
They overflowed waters over head my I said I have been cut off.
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
I called name your O Yahweh from a pit of lowest parts.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Voice my you heard may not you hide ear your to relief my to cry for help my.
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
You drew near on [the] day [when] I called on you you said may not you fear.
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
You have conducted O Lord [the] cases of self my you have redeemed life my.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
You have seen O Yahweh oppression my judge! judgment my.
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
You have seen all vengeance their all plans their to me.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
You have heard reproach their O Yahweh all plans their on me.
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
[the] lips of [those who] rise against Me and muttering their on me all the day.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Sitting their and rising their look at! I [am] mocking song their.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
You will repay to them recompense O Yahweh according to [the] work of hands their.
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
You will give to them shamelessness of heart curse your [may it belong] to them.
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
You will pursue [them] in anger and you will destroy them from under [the] heavens of Yahweh.

< Makoki 3 >