< Makoki 3 >
1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
I, am the man, that hath seen affliction, by the rod of his indignation;
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Me, hath he driven out and brought into darkness, and not light;
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Surely, against me, doth he again and again, turn his hand all the day.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
He hath worn out my flesh and my skin, hath broken my bones;
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
He hath built up against me, and carried round me, fortifications and a trench;
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
In dark places, hath he made me sit, like the dead of age-past times.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
He hath walled up around me, that I cannot get out, hath weighted my fetter;
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Yea, when I make outcry and implore, he hath shut out my prayer;
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
He hath walled in my ways with hewn stone, my paths, hath he caused to wind back.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
A bear lying in wait, he is to me, a lion, in secret places;
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
My ways, hath he turned aside, and hath torn me in pieces, hath made me desolate;
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
He hath trodden his bow, and set me up, as a mark for the arrow.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
He hath caused to enter my reins, the sons of his quiver;
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
I have become a derision to all my people, their song all the day;
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
He hath sated me with bitter things, hath drenched me with wormwood.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
And he hath crushed, with gravel-stones, my teeth, hath made me cower in ashes;
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
And thou hast thrust away from welfare, my soul, I have forgotten prosperity;
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
And I said, Vanished is mine endurance, even mine expectation, from Yahweh.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Remember my humiliation and my fleeings, the wormwood and poison;
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Thou wilt, indeed remember, that, bowed down concerning myself, is my soul;
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
This, will I bring back to my heart, therefore, will I hope.
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
The lovingkindnesses of Yahweh, verily they are not exhausted, Verily! not at an end, are his compassions:
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
New things for the mornings! Abundant is thy faithfulness:
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
My portion, is Yahweh, saith my soul, For this cause, will I wait for him.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Good is Yahweh, to them who wait for him, to the soul that will seek him;
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Good it is—both to wait and to be silent, for the deliverance of Yahweh;
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Good it is for a man, that he should bear the yoke in his youth.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Let him sit alone, and keep silence, because he took it upon himself:
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Let him put, in the dust, his mouth, peradventure, there is hope!
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Let him give, to him that smiteth him, his cheek, let him be sated with reproach.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Surely My Lord, will not cast off, unto times age-abiding;
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
Surely, though he cause grief, yet will he have compassion, according to the multitude of his lovingkindnesses;
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Surely he hath not afflicted from his heart, nor caused sorrow to the sons of men.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
To crush, under his feet, any of the prisoners of the earth;
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
To turn aside the right of a man, before the face of the Most High;
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
To oppress a son of earth in his cause, My Lord, hath made no provision.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Who was it that spake, and it was done, [when], My Lord, had not commanded?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
Out of the mouth of the Most High, Proceed there not misfortunes and blessing?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Why should a living son of earth complain, [Let] a man [complain] because of his sins?
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Let us search out our ways, and examine them well, and let us return unto Yahweh;
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Let us lift up our heart, to the opened palms, to the Mighty One in the heavens;
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
We, have trespassed and rebelled, Thou, hast not pardoned.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Thou hast covered thyself with anger, and pursued us, hast slain—hast not spared;
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Thou hast screened thyself with the clouds, that prayer, should not pass through;
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Offscouring and refuse, dost thou make us, in the midst of the peoples.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
With their mouth, opened wide over us, [stand] all our foes.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Terror and a pit, have befallen us, tumult and grievous injury;
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
With streams of water, mine eye runneth down, over the grievous injury of the daughter of my people.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Mine eye, poureth itself out and ceaseth not, without relief;
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
Until Yahweh out of the heavens shall look forth, and see,
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Mine eye dealeth severely with my soul, because of all the daughters of my city.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
They, have laid snares, for me as a bird, who are mine enemies without cause:
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
They have cut off, in the dungeon, my life, and have cast a stone upon me;
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Waters, flowed over, my head, I said, I am cut off!
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
I have called upon thy Name, O Yahweh, out of the dungeon below;
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
My voice, thou hast heard, —do not close thine ear to my respite, to mine outcry;
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Thou drewest near, in the day I kept calling on thee, thou saidst, Do not fear!
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Thou hast pleaded, O My Lord, the pleas of my soul, hast redeemed my life;
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Thou hast beheld, O Yahweh, my failure to get justice, Pronounce thou my sentence;
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Thou hast seen all their vindictiveness, all their plots against me.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Thou hast heard their reproach, O Yahweh, all their plots against me;
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
The lips of mine assailants, and their mutterings, are against me, all the day;
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
On their downsitting and their uprising, do thou look, I, am their song.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Thou wilt render to them a recompense, O Yahweh, according to the work of their hands;
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Thou wilt suffer them a veiling of heart, thy curse to them;
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Thou wilt pursue in anger, and wilt destroy them, from under the heavens of Yahweh.