< Makoki 3 >

1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Teg er den Mand, som saa Elendighed ved hans Vredes Ris.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Mig ledede og førte han ind i Mørke og ikke til Lys.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Kun imod mig vendte han atter og atter sin Haand den ganske Dag.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Han gjorde mit Kød og min Hud gammel; han sønderbrød mine Ben.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Han byggede imod mig og omgav mig med Galde og Møje.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
Han lod mig bo i de mørke Steder som dem, der ere døde i al Evighed.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Han tilmurede for mig, og jeg kan ikke komme ud, han gjorde min Lænke svar.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Naar jeg end skriger og raaber, lukker han til for min Bøn.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
Han har tilmuret mine Veje med hugne Stene, han har gjort mine Stier krogede.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Han er bleven mig som en Bjørn, der ligger paa Lur, som en Løve i Skjul.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Han lod mine Veje bøje af, og saa sønderrev han mig; han lagde mig øde.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
Han spændte sin Bue og stillede mig som Maalet for Pilen.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
Han lod Pile af sit Kogger trænge ind i mine Nyrer.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
Jeg er bleven alt mit Folk til Latter, deres Spottesang den ganske Dag.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Han mættede mig med beske Urter, „han gav mig rigelig Malurt at drikke
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
og lod mine Tænder bide i Grus, han nedtrykte mig i Aske.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
Og du bortstødte min Sjæl fra Fred, jeg har glemt det gode.
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
Og jeg sagde: Borte er min Kraft, og hvad jeg forventede fra Herren.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Kom min Elendighed og min Landflygtighed i Hu: Malurt og Galde!
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Min Sjæl kommer det ret i Hu og er nedbøjet i mit Indre.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Dette vil jeg tage mig til Hjerte, derfor vil jeg haabe:
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
Det er Herrens Miskundhed, at vi ikke ere fortærede; thi hans Barmhjertighed har ingen Ende.
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
Den er ny hver Morgen, din Trofasthed er stor.
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
Herren er min Del, siger min Sjæl, derfor vil jeg haabe til ham.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Herren er god imod dem, som bie efter ham, imod den Sjæl, som spørger efter ham.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Det er godt, at man haaber og er stille til Herrens Frelse.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Det er en Mand godt, at han bærer Aag i sin Ungdom.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Han vil sidde ene og tie; thi han lægger det paa ham.
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Han vil trykke sin Mund imod Støvet, om der maaske kunde være Forhaabning.
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Han vil vende Kinden imod den, som slaar ham, han vil mættes med Forhaanelse.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Thi Herren skal ikke forkaste evindelig.
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
Thi dersom han bedrøver, da skal han dog forbarme sig efter sin store Miskundhed.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Thi det er ikke af sit Hjerte, at han plager og bedrøver Menneskens Børn.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
For at knuse alle de bundne paa Jorden under sine Fødder,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
for at bøje en Mands Ret for den Højestes Ansigt,
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
for at forvende et Menneskes Retssag — skuer Herren ikke ned.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Hvo er den, som har sagt noget, saa at det skete, uden at Herren befaler det?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
Mon Lykke og Ulykke ikke udgaa af den Højestes Mund?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Hvorfor klager et Menneske som lever? — enhver for sine Synder!
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Lader os ransage vore Veje og efterspore dem og vende om til Herren!
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Lader os opløfte vort Hjerte tillige med vore Hænder til Gud i Himmelen!
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
Vi, vi have syndet og været genstridige, du tilgav ikke.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Du tildækkede os med Vrede og forfulgte os, ihjelslog, sparede ikke,
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Du skjulte dig med en Sky, at ingen Bøn kunde trænge igennem.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Du gjorde os til Skarn og Udskud midt iblandt Folkene.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Alle vore Fjender opspilede deres Mund imod os.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Der var Forfærdelse og Gru for os, Ødelæggelse og Undergang.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Mit Øje rinder med Vandbække over mit Folks Datters Undergang.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Mit Øje strømmer og bliver ikke stille, der er ingen Afladelse,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
indtil Herren skuer ned og ser til fra Himmelen.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Mit Øje voldte min Sjæl Smerte over alle min Stads Døtre.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Hart jagede mig som en Fugl de, der vare mine Fjender uden Grund.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
De bragte mit Liv til at vorde stille i Graven og kastede en Sten over mig.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Der strømmede Vand ned over mit Hoved, jeg sagde: Det er forbi med mig.
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
Jeg kaldte paa dit Navn, Herre! fra Graven, i det dybe.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Du har hørt min Røst; tilluk ej dit Øre for mit Suk, for mit Raab!
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Du holdt dig nær den Dag, jeg kaldte paa dig, du sagde: Frygt ikke!
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Herre! du har udført min Sjæls Sag, du har udløst mit Liv.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Herre! du har set den Uret, som sker mig, døm i min Sag!
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Du har set al deres Hævn, alle deres Tanker imod mig.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Herre! du har hørt deres haanende Tale, alle deres Tanker imod mig,
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
mine Modstanderes Ord og deres Anslag imod mig den ganske Dag.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Sku, hvorledes de sidde, og hvorledes de staa op; jeg er deres Spottesang.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Du skal gengælde dem, Herre! efter deres Hænders Gerning.
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Du skal give dem et Dække over Hjertet, din Forbandelse hører dem til.
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Du skal forfølge dem i Vrede, og ødelægge dem, at de ikke ere under Herrens Himmel.

< Makoki 3 >