< Makoki 3 >

1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Já jsem muž okoušející trápení od metly rozhněvání Božího.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Zahnal mne, a uvedl do tmy a ne k světlu.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Toliko proti mně se postavuje, a obrací ruku svou přes celý den.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Uvedl sešlost na tělo mé a kůži mou, a polámal kosti mé.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Zastavěl mne a obklíčil přeodpornou hořkostí.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
Postavil mne v tmavých místech jako ty, kteříž již dávno zemřeli.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Ohradil mne, abych nevyšel; obtížil ocelivý řetěz můj.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
A jakžkoli volám a křičím, zacpává uši před mou modlitbou.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
Ohradil cesty mé tesaným kamenem, a stezky mé zmátl.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Jest nedvěd číhající na mne, lev v skrejších.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Cesty mé stočil, anobrž roztrhal mne, a na to mne přivedl, abych byl pustý.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
Natáhl lučiště své, a vystavil mne za cíl střelám.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
Postřelil ledví má střelami toulu svého.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
Jsem v posměchu se vším lidem svým, a písničkou jejich přes celý den.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Sytí mne hořkostmi, opojuje mne pelynkem.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
Nadto potřel o kameníčko zuby mé, vrazil mne do popela.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
Tak jsi vzdálil, ó Bože, duši mou od pokoje, až zapomínám na pohodlí,
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
A říkám: Zahynulatě síla má i naděje má, kterouž jsem měl v Hospodinu.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
A však duše má rozvažujíc trápení svá a pláč svůj, pelynek a žluč,
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Rozvažujíc to ustavičně, ponižuje se ve mně.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
A přivodě sobě to ku paměti, (naději mám),
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
Že veliké jest milosrdenství Hospodinovo, když jsme do konce nevyhynuli. Nepřestávajíť zajisté slitování jeho,
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
Ale nová jsou každého jitra; převeliká jest pravda tvá.
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
Díl můj jest Hospodin, říká duše má; protož naději mám v něm.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Dobrý jest Hospodin těm, jenž očekávají na něj, duši té, kteráž ho hledá.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Dobré jest trpělivě očekávajícímu na spasení Hospodinovo.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Dobré jest muži tomu, kterýž by nosil jho od dětinství svého,
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Kterýž by pak byl opuštěn, trpělivě se má v tom, což na něj vloženo,
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Dávaje do prachu ústa svá, až by se ukázala naděje,
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Nastavuje líce tomu, kdož jej bije, a sytě se potupou.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Neboť nezamítá Pán na věčnost;
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
Nýbrž ačkoli zarmucuje, však slitovává se podlé množství milosrdenství svého.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Netrápíť zajisté z srdce svého, aniž zarmucuje synů lidských.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
Aby kdo potíral nohama svýma všecky vězně v zemi,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
Aby nespravedlivě soudil muže před oblíčejem Nejvyššího,
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
Aby převracel člověka v při jeho, Pán nelibuje.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Kdo jest, ješto když řekl, stalo se něco, a Pán nepřikázal?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
Z úst Nejvyššího zdali nepochází zlé i dobré?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Proč by tedy sobě stýskal člověk živý, muž nad kázní za hříchy své?
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Zpytujme raději a ohledujme cest našich, a navraťme se až k Hospodinu.
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Pozdvihujme srdcí i rukou svých k Bohu silnému v nebe.
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
Myť jsme se zpronevěřili, a zpurní jsme byli, protož ty neodpouštíš.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Obestřels se hněvem a stiháš nás, morduješ a nešanuješ.
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Obestřels se oblakem, aby nemohla proniknouti k tobě modlitba.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Za smeti a povrhel položil jsi nás u prostřed národů těchto.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Rozdírají na nás ústa svá všickni nepřátelé naši.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Strach a jáma potkala nás, zpuštění a setření.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Potokové vod tekou z očí mých pro potření dcery lidu mého.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Oči mé slzí bez přestání, proto že není žádného odtušení,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
Ažby popatřil a shlédl Hospodin s nebe.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Oči mé rmoutí duši mou pro všecky dcery města mého.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Loviliť jsou mne ustavičně, jako ptáče, nepřátelé moji bez příčiny.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
Uvrhli do jámy život můj, a přimetali mne kamením.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Rozvodnily se vody nad hlavou mou, řekl jsem: Jižtě po mně.
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
Vzývám jméno tvé, ó Hospodine, z jámy nejhlubší.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Hlas můj vyslýchával jsi; nezacpávejž ucha svého před vzdycháním mým a voláním mým.
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
V ten den, v němž jsem tě vzýval, přicházeje, říkávals: Neboj se.
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Pane, zasazuje se o při duše mé, vysvobozoval jsi život můj.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Vidíš, ó Hospodine, převrácenost, kteráž se mně děje, dopomoziž mi k spravedlnosti.
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Vidíš všecko vymstívání se jejich, všecky úklady jejich proti mně.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Slýcháš utrhání jejich, ó Hospodine, i všecky obmysly jejich proti mně,
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
Řeči povstávajících proti mně, a přemyšlování jejich proti mně přes celý den.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Pohleď, jak při sedání jejich i povstání jejich jsem písničkou jejich.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Dej jim odplatu, Hospodine, podlé díla rukou jejich.
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Dej jim zatvrdilé srdce a prokletí své na ně.
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Stihej v prchlivosti, a vyhlaď je, ať nejsou pod nebem tvým.

< Makoki 3 >