< Makoki 2 >

1 Yadda Ubangiji ya rufe Diyar Sihiyona da gizagizan fushi! Ya jefar da darajar Isra’ila daga sama zuwa ƙasa; bai tuna da wurin ɗora ƙafafunsa ba a ranar fushinsa.
Huru hafver Herren förmörkrat dottrena Zion med sine vrede? Han hafver kastat Israels härlighet af himmelen neder på jordena; han hafver icke tänkt uppå sin fotapall, i sine vredes dag.
2 Ubangiji ya hallakar da wurin zaman Yaƙub ba tausayi; A cikin fushinsa kuma zai rurrushe kagaran Diyar Yahuda. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulki.
Herren hafver utan barmhertighet alla Jacobs boningar förlagt; han hafver i sine grymhet afbrutit dottrenes Juda fäste, och slagit dem omkull, han hafver oskärat både hennes rike och hennes Förstar.
3 A cikin zafin fushi ya fasa kowane ƙaho na Isra’ila. Ya janye hannun damansa sa’ad da maƙiyi ya zo. Ya yi ƙuna a cikin Yaƙub kamar wuta mai ƙone duk abin da yake kusa da ita.
Han hafver sönderbrutit Israels starkhet uti sine grymma vrede; han hafver dragit sina högra hand tillbaka, då fienden kom, och hafver upptändt en eld i Jacob, den allt omkring förtärer.
4 Kamar abokin gāba, ya ɗana bakansa; hannun damansa na shirye. Kamar maƙiyi, ya kashe duk wanda idonsa ya ji daɗin gani; ya zuba fushinsa kamar wuta a kan tenti na Diyar Sihiyona.
Han hafver spänt sin båga, lika som en fiende; sina högra hand hafver han fört såsom en ovän, och dräpit allt det som lustigt var till seendes, och utgjutit sina grymnet, lika som en eld uti dottrenes Zions hyddo.
5 Ubangiji kamar maƙiyi ne; ya hallaka Isra’ila. Ya hallaka wurarenta duka ya kuma hallaka kagaranta. Ya ƙara yawan makoki da baƙin ciki wa Diyar Yahuda.
Herren är lika som en fiende; han hafver omstört Israel, han hafver omstört alla hans palats, och förderfvat hans fäste; han hafver gjort dottrene Juda mycken klagan och sorg.
6 Ya rushe haikalinsa kamar lambu; ya hallaka wurin yi masa sujada. Ubangiji ya sa Sihiyona ta manta da bukukkuwanta da kuma ranakunta na Asabbaci; a cikin zafin fushinsa ya watsar da sarki da firist.
Han hafver uppgrafvit hans tjäll, lika som en örtegård, och förderfvat hans boning; Herren hafver låtit förgäta i Zion både helgedag och Sabbath, och låtit i sine grymma vrede skämma både Konung och Prest.
7 Ubangiji ya ƙi bagadensa ya kuma yi wofi da haikalinsa. Ya ba maƙiyinta fadodinta; suka yi sowa a cikin gidan Ubangiji kamar a ranar da ake yin biki.
Herren hafver förkastat sitt altare, och tillspillogifvit sin helgedom; han hafver gifvit hans palats murar uti fiendans händer, så att de hafva ropat i Herrans hus, lika som uppå enom helgedag.
8 Ubangiji ya ƙuduri niyya yă rushe bangon da yake kewaye da Diyar Sihiyona. Ya auna da igiyar awo bai fasa hallaka ta ba. Ya sa katanga da katanga duk suka lalace.
Herren tänkte till att förderfva dottrenes Zions murar; han drog snöret deröfver, och icke afvände sina hand, tilldess han henne förderfvade; tornen stå ömkeliga, och muren ligger jämmerliga.
9 Ƙofofinta sun nutse a cikin ƙasa; ya kakkarya ƙarafanta. Sarakunanta da’ya’yan sarakunanta duk an kai su bauta cikin waɗansu ƙasashe, babu sauran doka, annabawa kuma ba su samun wahayi daga wurin Ubangiji.
Hans portar ligga djupt neder i jordene; hans bommar hafver han sönderbrutit, och tillintetgjort; hans Konungar och Förstar äro ibland Hedningarna, der de intet kunna öfva lagen, och hans Propheter hafva ingen syn af Herranom.
10 Dattawan Diyar Sihiyona sun zauna shiru a ƙasa; suka kuma sa rigar buhu.’Yan matan Urushalima suka sunkuyar da kawunansu ƙasa.
Dottrenes Zions äldste ligga på jordene, och äro tyste; de kasta stoft uppå sin hufvud, och hafva dragit säcker uppå sig Jerusalems jungfrur hänga deras hufvud neder åt jordene.
11 Idanuna sun dushe don yawan kuka, raina na cike da baƙin ciki; zuciyata ta karaya domin mutanena sun hallaka, domin yara da jarirai suna suma a kan hanyoyi a cikin birni.
Jag hafver nästan gråtit mig ögonen ut, så att det gör mig ondt i mitt lif; min lefver är utgjuten uppå jordena, öfver mins folks dotters jämmer, då spenabarn och öfvermagar försmäktades på gatomen i stadenom;
12 Suna ce wa uwayensu, “Ina burodi da ruwan inabi?” Yayinda suke suma kamar mutanen da aka ji masu ciwo a cikin birni, sa’ad da suke mutuwa a hannuwan uwayensu.
Då de sade till sina mödrar: Hvar är bröd och vin? då de försmäktades på gatomen i stadenom, såsom de der dödssåre voro, och uppgåfvo sin anda i deras mödrars famn.
13 Me zan ce miki? Da me zan kwatanta ki, ke Diyar Urushalima? Da me zan misalta ki, yadda zan iya yi miki ta’aziyya, Ke Budurwa Diyar Sihiyona? Ciwonki yana da zurfi kamar teku. Wane ne zai iya warkar da ke?
O du dotter Jerusalem, hvem skall jag likna dig vid? Och för hvad skall jag hålla dig, du jungfru dotter Zion? Vid hvad skall jag likna dig, der jag dig med trösta måtte. Ty din skade är stor, lika som ett haf; ho kan hela dig?
14 Wahayin annabawanki ƙarya ne kuma marasa amfani; ba su tona zunubanki ba yadda za su iya ceto ki daga bauta ba. Sun yi miki annabcin ƙarya marar amfani.
Dine Propheter hafva dig predikat lösa och dåraktiga syner, och icke uppenbarat dig dina missgerning, der de med måtte förtagit dig ditt fängelse; utan hafva predikat dig lösa predikan, på det de skulle predika dig utu landena.
15 Duk masu wucewa suna yi miki tafi na reni; suna yi wa Diyar Urushalima tsaki suna kaɗa kai suna cewa, “Wannan ne birnin da aka ce kyakkyawa ne, mai farantawa dukan duniya rai?”
Alle de som der framom gå, de klappa med händerna, hvissla åt dig, och rista hufvudet öfver dottrena Jerusalem: Är detta den staden, der man af säger, att han är den aldraskönaste, af hvilkom allt landet gläder sig?
16 Maƙiyanki duka suna ta surutu game da ke; suna tsaki suna cizon haƙora suna cewa, “Mun hallaka ta. Wannan ce ranar da muke jira; yau mun gan ta.”
Alle dine fiender gapa med munnen emot dig; hvissla till dig, gnissla med tänderna, och säga: Huj, vi hafve förderfvat honom; detta är den dagen, som vi begärat hafve; vi hafve fått det, vi hafve lefvat så länge.
17 Ubangiji ya yi abin da ya shirya; ya cika maganarsa, wadda ya umarta tun daɗewa. Ya jefar da ke ba tausayi, ya bari maƙiya sun yi nasara da ke, ya ɗaukaka ƙahon maƙiyanki.
Herren hafver gjort det han i sinnet hade; han hafver fullkomnat sitt ord, som han långt tillförene budit hade; han hafver förderfvat utan barmhertighet; han hafver fröjdat fiendan öfver dig, och upphöjt dina ovänners magt.
18 Zuciyar mutane ta yi kuka ga Ubangiji. Ya bangon Diyar Urushalima, bar hawayenki su zuba kamar rafi dare da rana; kada ki huta, kada idanunki su huta.
Deras hjerto ropade till Herran: O du dottrenes Zions mur, låt tårar flyta både dag och natt, lika som en bäck; håll intet upp, och din ögnasten vände intet åter.
19 Ki tashi, ki yi kuka cikin dare, dare na yi sai ki fara kuka; kina buɗewa Ubangiji zuciyarki. Ki ɗaga hannuwanki gare shi domin rayukan’ya’yanki, waɗanda suka suma don yunwa a kan kowane titi.
Statt upp om nattena, och ropa; utgjut ditt hjerta i första väktene inför Herranom, lika som vatten; lyft upp dina händer till honom, för din unga barns själar, som af hunger dö i all gatomot.
20 “Ka duba, ka gani ya Ubangiji. Wane ne ka taɓa yi wa haka? Ko ya kamata uwaye su ci’ya’yansu,’ya’yan da suka yi reno? Ko ya kamata a kashe firistoci da annabawa a cikin haikalin Ubangiji?
Herre, skåda dock; och se till hvem du så förderfvat hafver. Skola nu qvinnorna äta sin lifsfrukt, de yngsta barnen, som näppliga en spann lång äro? Skola Propheterna och Presterna uti Herrans helgedom så dräpne varda?
21 “Matasa da tsofaffi duk suna kwanciya a cikin ƙurar tituna; an karkashe matasa da’yan matana da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka; ka kashe su ba tausayi.
På gatorna, neder på jordene, lågo både unge och gamle; mina jungfrur och ynglingar, äro fallne genom svärd; du hafver dräpit på dine vredes dag, du hafver slagtat utan barmhertighet.
22 “Kamar yadda kake yin gayyata a ranar biki, haka kake kawo mini tsoro a kowane gefe. A ranar fushin Ubangiji ba mai tserewa ba wanda zai tsira; maƙiyina ya kashe waɗanda na yi renonsu, na kuma lura da su.”
Du hafver kallat mina fiendar allt omkring, lika som till en helgedag, så att på Herrans vredes dag ingen undsluppen och igenlefd är; de som jag uppfödt och uppfostrat hafver, dem hafver fienden förgjort.

< Makoki 2 >