< Makoki 2 >
1 Yadda Ubangiji ya rufe Diyar Sihiyona da gizagizan fushi! Ya jefar da darajar Isra’ila daga sama zuwa ƙasa; bai tuna da wurin ɗora ƙafafunsa ba a ranar fushinsa.
Oh how hath the Lord covered in his anger the daughter of Zion with a cloud; he hath cast down from heaven unto the earth the ornament of Israel; and he hath not remembered his footstool on the day of his anger!
2 Ubangiji ya hallakar da wurin zaman Yaƙub ba tausayi; A cikin fushinsa kuma zai rurrushe kagaran Diyar Yahuda. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulki.
The Lord hath destroyed and hath not pitied all the habitation of Jacob: he hath thrown down in his wrath the strong-holds of the daughter of Judah: he hath thrown them down to the ground; he hath defiled the kingdom and its princes.
3 A cikin zafin fushi ya fasa kowane ƙaho na Isra’ila. Ya janye hannun damansa sa’ad da maƙiyi ya zo. Ya yi ƙuna a cikin Yaƙub kamar wuta mai ƙone duk abin da yake kusa da ita.
He hath hewn away in his fierce anger the whole horn of Israel; he hath drawn back his right hand before the enemy; and he burnt against Jacob like a flaming fire, which devoureth round about.
4 Kamar abokin gāba, ya ɗana bakansa; hannun damansa na shirye. Kamar maƙiyi, ya kashe duk wanda idonsa ya ji daɗin gani; ya zuba fushinsa kamar wuta a kan tenti na Diyar Sihiyona.
He bent his bow like an enemy; he held out his right hand as an adversary, and slew all that were pleasant to the eye: in the tent of the daughter of Zion did he pour out like fire his fury.
5 Ubangiji kamar maƙiyi ne; ya hallaka Isra’ila. Ya hallaka wurarenta duka ya kuma hallaka kagaranta. Ya ƙara yawan makoki da baƙin ciki wa Diyar Yahuda.
The Lord became like an enemy; he destroyed Israel, he destroyed all her palaces, he ruined her strong-holds, and he increased in the midst of the daughter of Judah groaning and wailing.
6 Ya rushe haikalinsa kamar lambu; ya hallaka wurin yi masa sujada. Ubangiji ya sa Sihiyona ta manta da bukukkuwanta da kuma ranakunta na Asabbaci; a cikin zafin fushinsa ya watsar da sarki da firist.
And he violently wasted, as if it were a garden, his tabernacle; he destroyed his place of assembly: [yea, ] the Lord hath caused to be forgotten in Zion the solemn feast and the day of rest, and hath despised in the indignation of his anger both king and priest.
7 Ubangiji ya ƙi bagadensa ya kuma yi wofi da haikalinsa. Ya ba maƙiyinta fadodinta; suka yi sowa a cikin gidan Ubangiji kamar a ranar da ake yin biki.
The Lord hath cast off his altar, he hath made void his sanctuary, he hath surrendered into the hand of the enemy the walls of her palaces: they have made their voice to resound in the house of the Lord, as on a day of a solemn feast.
8 Ubangiji ya ƙuduri niyya yă rushe bangon da yake kewaye da Diyar Sihiyona. Ya auna da igiyar awo bai fasa hallaka ta ba. Ya sa katanga da katanga duk suka lalace.
The Lord hath resolved to destroy the wall of the daughter of Zion; he stretched out the measuring-line, he withdrew not his hand from destroying: and he caused the rampart and the wall to mourn; together they languish.
9 Ƙofofinta sun nutse a cikin ƙasa; ya kakkarya ƙarafanta. Sarakunanta da’ya’yan sarakunanta duk an kai su bauta cikin waɗansu ƙasashe, babu sauran doka, annabawa kuma ba su samun wahayi daga wurin Ubangiji.
Sunk into the ground are her gates, he hath ruined and broken her bars: her king and her princes are among the nations without any law; her prophets also obtain no more any vision from the Lord.
10 Dattawan Diyar Sihiyona sun zauna shiru a ƙasa; suka kuma sa rigar buhu.’Yan matan Urushalima suka sunkuyar da kawunansu ƙasa.
The elders of the daughter of Zion sit upon the ground, they keep silence: they have thrown dust upon their head; they have girt themselves with sackcloth: the virgins of Jerusalem have brought down low their head to the ground.
11 Idanuna sun dushe don yawan kuka, raina na cike da baƙin ciki; zuciyata ta karaya domin mutanena sun hallaka, domin yara da jarirai suna suma a kan hanyoyi a cikin birni.
My eyes do fail with tears, my bowels are heated, my liver is poured upon the earth because of the breach of the daughter of my people; because babes and sucklings faint away in the streets of the town.
12 Suna ce wa uwayensu, “Ina burodi da ruwan inabi?” Yayinda suke suma kamar mutanen da aka ji masu ciwo a cikin birni, sa’ad da suke mutuwa a hannuwan uwayensu.
To their mothers they say, Where is corn and wine? when they faint away like the deadly wounded in the streets of the city, when their soul is poured out on the bosom of their mother.
13 Me zan ce miki? Da me zan kwatanta ki, ke Diyar Urushalima? Da me zan misalta ki, yadda zan iya yi miki ta’aziyya, Ke Budurwa Diyar Sihiyona? Ciwonki yana da zurfi kamar teku. Wane ne zai iya warkar da ke?
What shall I take to witness for thee? what shall I compare unto thee, O daughter of Jerusalem? what shall I find equal to thee, that I may comfort thee, O virgin daughter of Zion? for great like the sea is thy breach; who can bring healing to thee?
14 Wahayin annabawanki ƙarya ne kuma marasa amfani; ba su tona zunubanki ba yadda za su iya ceto ki daga bauta ba. Sun yi miki annabcin ƙarya marar amfani.
Thy prophets foresaw for thee vain and deceptive things; and they did not lay open thy iniquity, to cause thy backsliders to return: but they foresaw for thee prophecies of falsehood and seduction.
15 Duk masu wucewa suna yi miki tafi na reni; suna yi wa Diyar Urushalima tsaki suna kaɗa kai suna cewa, “Wannan ne birnin da aka ce kyakkyawa ne, mai farantawa dukan duniya rai?”
All that pass by [this] way clap their hands on account of thee; they hiss and shake their head over the daughter of Jerusalem: [saying, ] Is this the city that men called The perfection of beauty. The joy for all the earth?
16 Maƙiyanki duka suna ta surutu game da ke; suna tsaki suna cizon haƙora suna cewa, “Mun hallaka ta. Wannan ce ranar da muke jira; yau mun gan ta.”
All thy enemies open wide their mouth against thee; they hiss and gnash their teeth; they say, We have swallowed her up: ah, truly this is the day that we hoped for; we have found, we have seen it.
17 Ubangiji ya yi abin da ya shirya; ya cika maganarsa, wadda ya umarta tun daɗewa. Ya jefar da ke ba tausayi, ya bari maƙiya sun yi nasara da ke, ya ɗaukaka ƙahon maƙiyanki.
The Lord hath done what he had resolved; he hath accomplished his word which he had ordained already in the days of old; he hath thrown down, and hath not pitied; and he hath caused to rejoice over thee thy enemy, he hath raised on high the horn of thy adversaries.
18 Zuciyar mutane ta yi kuka ga Ubangiji. Ya bangon Diyar Urushalima, bar hawayenki su zuba kamar rafi dare da rana; kada ki huta, kada idanunki su huta.
Their heart crieth unto the Lord, O thou wall of the daughter of Zion, let tears run down like a stream day and night; allow thyself no rest; let not the apple of thy eye be still.
19 Ki tashi, ki yi kuka cikin dare, dare na yi sai ki fara kuka; kina buɗewa Ubangiji zuciyarki. Ki ɗaga hannuwanki gare shi domin rayukan’ya’yanki, waɗanda suka suma don yunwa a kan kowane titi.
Arise, complain aloud in the night, in the beginning of the watches; pour out like water thy heart before the face of the Lord: lift up toward him thy hands because of the life of thy babes, that faint away for hunger at the corner of all the streets.
20 “Ka duba, ka gani ya Ubangiji. Wane ne ka taɓa yi wa haka? Ko ya kamata uwaye su ci’ya’yansu,’ya’yan da suka yi reno? Ko ya kamata a kashe firistoci da annabawa a cikin haikalin Ubangiji?
See, O Lord, and behold! to whom hast thou ever done the like? Shall women, then, eat their own fruit, the babes they have tenderly nursed? or shall there be slain in the sanctuary of the Lord the priest and the prophet?
21 “Matasa da tsofaffi duk suna kwanciya a cikin ƙurar tituna; an karkashe matasa da’yan matana da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka; ka kashe su ba tausayi.
There lie down on the ground in the streets the lad and the ancient: my virgins and my young men are fallen by the sword: thou hast slain on the day of thy anger; thou hast slaughtered, thou hast not pitied.
22 “Kamar yadda kake yin gayyata a ranar biki, haka kake kawo mini tsoro a kowane gefe. A ranar fushin Ubangiji ba mai tserewa ba wanda zai tsira; maƙiyina ya kashe waɗanda na yi renonsu, na kuma lura da su.”
Thou hast called, as it were on a festive day, my evil neighbors from round about; and there was not on the day of the Lord's anger one that escaped or remained: those that I had tenderly nursed and reared up my enemy brought to their end.