< Makoki 1 >

1 Yanzu birnin ya zama babu kowa a ciki, birnin da a dā yake cike da mutane! Yanzu birnin ya zama kamar gwauruwa, wadda a dā babba ce ita a cikin ƙasashe! Ita da take sarauniya a cikin larduna yanzu ta zama baiwa.
اورشلیم که زمانی شهری پرجمعیت بود اینک متروک شده است! شهری که در بین قومها محبوب بود اینک بیوه گشته است! او که ملکهٔ شهرها بود اکنون برده شده است!
2 Tana yin kuka mai zafi da dare, hawaye na gangara a kan kumatunta. A cikin masoyanta duka babu wanda ya yi mata ta’aziyya. Duk abokanta sun yashe ta; sun zama abokan gābanta.
اورشلیم تمام شب می‌گرید و قطره‌های اشک روی گونه‌هایش می‌غلتند. از میان یارانش یکی هم باقی نمانده که او را تسلی دهد. دوستانش به او خیانت کرده و همگی با او دشمن شده‌اند.
3 Bayan wahala da baƙin ciki, Yahuda ta tafi bauta. Ta zauna a cikin ƙasashe, ba tă samu wurin hutawa ba. Duk masu fafararta sun same ta sa’ad da take cikin matuƙar ɓacin rai.
مردم مصیبت‌زده و رنجدیدهٔ یهودا به اسارت رفته‌اند؛ به دیار غربت تبعید شده‌اند و اینک هیچ آسایش ندارند. دشمنان، آنها را احاطه نموده عرصه را بر آنها تنگ کرده‌اند.
4 Hanyoyin zuwa Sihiyona suna makoki, gama ba wanda ya zo bikin da ta shirya. Ba kowa a hanyoyin shiganta. Firistocinta suna gurnani,’yan matana kuma suna wahala, kuma tana cikin shan wahala ƙwarai.
راههای اورشلیم ماتم گرفته‌اند، زیرا دیگر مردم نمی‌آیند تا در روزهای عید عبادت کنند. دروازه‌های شهر ساکتند، کاهنانش آه می‌کشند و دوشیزگانش عزادارند. اورشلیم در اضطراب و تلخکامی فرو رفته است.
5 Maƙiyanta sun zama shugabanninta; Abokan gābanta suna da kwanciyar rai. Ubangiji ya kawo mata ɓacin rai domin yawan zunubanta.’Ya’yanta sun tafi bauta, a ƙarƙashin maƙiyanta.
دشمنانش سَروَرِ او شده‌اند و خصمانش در آسایش‌اند. خداوند اورشلیم را برای گناهان بسیارش تنبیه کرده است. دشمنان، فرزندان او را اسیر کرده، به دیار غربت به بردگی برده‌اند.
6 Diyar Sihiyona ba ta da sauran daraja.’Ya’yan sarakunanta sun zama kamar bareyi waɗanda suka rasa wurin kiwo; cikin rashin ƙarfi suka guje wa masu fafararsu.
تمام شکوه و زیبایی اورشلیم از دست رفته است. بزرگانش مانند غزالهای گرسنه دنبال چراگاه می‌گردند و ناتوانتر از آنند که بتوانند از چنگ دشمن فرار کنند.
7 A cikin kwanakin da take shan wahala take kuma yawo Urushalima ta tuna da dukan dukiyar da take da ita a kwanakin dā can. Sa’ad da mutanenta suka faɗa cikin hannun abokan gābanta, ba wanda ya taimake ta. Maƙiyanta suka dube ta suka yi mata dariya don hallakar da ta auko mata.
اینک اورشلیم در میان مصیبتها، روزهای پرشکوه گذشته را به یاد می‌آورد. زمانی که او به محاصرهٔ دشمن درآمد، هیچ مدد کننده‌ای نداشت؛ دشمن او را مغلوب کرد و به شکست او خندید.
8 Urushalima ta yi zunubi ƙwarai saboda haka ta zama marar tsarki. Dukan masu martaba ta sun raina ta, gama sun ga tsiraicinta; ita ma da kanta tana nishi da ƙyar ta kuma juya baya.
اورشلیم گناهان بسیاری مرتکب شده و ناپاک گردیده است. تمام کسانی که او را تکریم می‌کردند، اینک تحقیرش می‌کنند، زیرا برهنگی و خواری او را دیده‌اند. او می‌نالد و از شرم، چهرهٔ خود را می‌پوشاند.
9 Ƙazantarta ta manne wa rigunanta; ba tă kula da nan gaba ba, fāɗuwarta kuwa babban abu ne; babu wanda zai yi mata ta’aziyya. “Duba, ya Ubangiji, ka ga wahalata, gama maƙiyi ya yi nasara.”
لکهٔ ننگی بر دامن اورشلیم بود، اما او اعتنایی نکرد؛ او به عاقبت خود نیاندیشید و ناگهان سقوط کرد. اینک کسی نیست که او را تسلی دهد. او فریاد برمی‌آورد، «خداوندا، به مصیبتم نگاه کن، زیرا دشمن بر من پیروز شده است.»
10 Maƙiya ya kwashe dukiyarta duka; ta ga mutanen da ba su san Allah ba sun shiga wuri mai tsarkinta waɗanda ka hana su shiga taron jama’arka.
دشمن، گنجینه‌های او را غارت کرد و قومهای بیگانه در برابر چشمانش به عبادتگاه مقدّسش داخل شدند، قومهایی که خدا ورود آنها را به عبادتگاهش قدغن کرده بود.
11 Dukan mutanenta suna nishi da ƙyar suna neman burodi; sun sayar da dukiyarsu don su samu abinci don kada su mutu da yunwa. “Ubangiji, ka duba ka gani, gama an yashe ni.”
اهالی اورشلیم برای یک لقمه نان آه می‌کشند. هر چه داشتند برای خوراک دادند تا زنده بمانند. اورشلیم می‌گوید: «خداوندا، ببین چگونه خوار شده‌ام!
12 “Ko wannan ba wani abu ba ne a wurinku, dukanku masu wucewa? Ku duba ku gani. Ko akwai wata wahala kamar irin wadda nake sha, wadda Ubangiji ya auko mini a cikin zafin fushinsa?
«ای کسانی که از کنارم می‌گذرید، چرا به من نگاه نمی‌کنید؟ نگاهی به من بیندازید و ببینید آیا غمی همچون غم من وجود دارد؟ ببینید خداوند به هنگام خشم خود به من چه کرده است!
13 “Daga sama ya aiko da wuta, ya aiko ta cikin ƙasusuwana. Ya shimfiɗa raga a ƙafafuna ya juyo da ni. Ya bar ni ni kaɗai, sumamme dukan yini.
«او از آسمان آتش فرستاد و تا مغز استخوان مرا سوزاند. سر راهم دام گسترد و مرا به زمین کوبید. او مرا در مصیبتم ترک گفت و در غمی بی‌پایان رهایم کرد.
14 “Ya ɗaura zunubaina a wuyana; aka naɗe su a hannuwansa. Aka rataye su a wuyana Ubangiji ya kwashe ƙarfina. Ya bashe ni ga waɗanda suka fi ni ƙarfi.
«گناهانم را به هم بافت و همچون طنابی بر گردنم انداخت و مرا زیر یوغ بردگی کشاند. تمام توانم را از من گرفت و مرا در چنگ دشمنانم که قویتر از من بودند رها کرد.
15 “Ubangiji ya ƙi duk mayaƙan da suke tare da ni; ya sa wata runduna ta tayar mini ta kuma tattake samarina. Ubangiji ya tattake budurwa Diyar Yahuda kamar’ya’yan inabi a wurin matsewa.
«خداوند تمام سربازان شجاع مرا از من گرفت. او لشکری بر ضد من فرا خواند تا جوانان مرا از بین ببرند. خداوند شهر محبوب خود را همچون انگور در چرخشت پایمال کرد.
16 “Dalilin da ya sa nake kuka ke nan idanuna kuma suna ta zubar da hawaye. Babu wani a kusa da zai yi mini ta’aziyya, ba wanda zai sabunta ruhuna.’Ya’yana sun zama fakirai domin maƙiyina ya yi nasara.”
«برای این مصیبتهاست که می‌گریم و قطره‌های اشک بر گونه‌هایم می‌غلتند. آن که به من دلداری می‌داد و جانم را تازه می‌ساخت از من دور شده است. دشمن بر من غالب آمده و فرزندانم بی‌کس شده‌اند.»
17 Sihiyona ta miƙa hannunta, amma ba wani da zai yi mata ta’aziyya. Ubangiji ya umarta cewa maƙwabtansa za su zama maƙiyansa; Urushalima ta zama abar ƙyama a cikinsu.
اورشلیم دستهای خود را دراز می‌کند و کمک می‌طلبد، اما کسی نیست که به دادش برسد. خداوند قومهای همسایه را بر ضد اسرائیل فرا خوانده است تا اورشلیم را همچون پارچه‌ای کثیف دور اندازند.
18 “Ubangiji mai adalci ne, duk da haka na yi tawaye da umarninsa. Ku saurara, jama’a duka; ku dubi wahalar da nake sha. Samarina da’yan matana duka sun tafi bauta.
«اما خداوند عادلانه حکم فرموده است، زیرا من از فرمان او سرپیچی کرده بودم. ای مردم جهان، اندوه مرا بنگرید و ببینید چگونه پسران و دخترانم را به اسیری برده‌اند.
19 “Na kira abokaina amma sun yashe ni. Firistocina da dattawana sun hallaka a cikin birnin yayinda suke neman abinci don kada su mutu da yunwa.
«از یاران کمک خواستم، اما ایشان به من خیانت کردند. کاهنان و ریش‌سفیدان در حالی که به دنبال لقمه نانی بودند تا خود را زنده نگه دارند، در کوچه‌های شهر از شدت گرسنگی جان دادند.
20 “Duba, Ubangiji, ka ga ƙuncin da nake ciki! Ina shan azaba a raina, ba ni da kwanciyar rai a cikin zuciyata, domin na yi tawaye sosai. A waje takobi na kisa; a ciki kuma akwai mutuwa.
«ای خداوند، ببین چقدر پریشان و نگرانم! به خاطر گناهانی که انجام داده‌ام جانم در عذاب است. در خانه، بلای کشنده در انتظارم است و در بیرون، شمشیر مرگبار.
21 “Mutane suna ji ina nishi da ƙyar, amma ba wanda zai yi mini ta’aziyya. Dukan maƙiyana sun ji wahalar da nake ciki; suna farin ciki da abin da ka yi. Ka kawo ranan nan da ka sanar domin su ma su zama kamar ni.
«مردم ناله‌هایم را می‌شنوند، اما کسی به دادم نمی‌رسد. دشمنانم چون شنیدند چه بلایی بر سرم آوردی، شاد شدند. ای خداوند، به وعده‌ات وفا کن و بگذار دشمنانم نیز به بلای من دچار گردند.
22 “Bari ka ga muguntarsu duka; ka yi musu yadda ka yi mini domin dukan zunubansu. Nishina da yawa kuma zuciyata ta gaji.”
«به گناهان آنها نیز نظر کن و همان‌گونه که مرا برای گناهانم تنبیه کرده‌ای، آنان را نیز به سزای کردارشان برسان. ناله‌های من بسیار و دلم بی‌تاب است.»

< Makoki 1 >