< Mahukunta 1 >

1 Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
Efter Josua död frågade Israels barn Herran, och sade: Ho skall ibland oss föra örliget emot de Cananeer?
2 Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
Herren sade: Juda skall föra det; si, jag hafver gifvit landet i hans hand.
3 Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
Då sade Juda till sin broder Simeon: Drag med mig upp i min lott, och låt oss strida emot de Cananeer, så vill jag åter draga med dig i din lott. Så drog Simeon med honom.
4 Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
Då nu Juda drog ditupp, gaf Herren honom de Cananeer och Phereseer i deras händer; och de slogo i Besek tiotusend män.
5 A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
Och de funno AdoniBesek i Besek; och stridde emot honom, och slogo de Cananeer och Phereseer.
6 Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
Men AdoniBesek flydde, och de jagade efter honom, fingo honom, och höggo af honom tummarna, både af hans händer och fötter.
7 Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
Då sade AdoniBesek: Sjutio Konungar, med afhuggna tummar af deras händer och fötter, hemtade upp under mitt bord; såsom jag nu gjort hafver, så hafver Gud vedergullit mig. Och de förde honom till Jerusalem, der blef han död.
8 Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
Men Juda barn stridde emot Jerusalem, och vunno det, och slogo det med svärdsegg, och brände staden upp.
9 Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
Sedan drogo Juda barn neder, till att strida emot de Cananeer, som bodde på bergen, och söderut, och i dalarna.
10 Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
Och Juda drog emot de Cananeer, som bodde i Hebron; men Hebron het i förtiden KiriathArba; och slog Sesai, och Ahiman, och Thalmai;
11 Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
Och drog dädan emot Debirs inbyggare; men Debir het i förtiden KiriathSepher.
12 Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
Och Caleb sade: Den som KiriathSepher slår och vinner, honom vill jag gifva mina dotter Achsa till hustru.
13 Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
Då vann det Athniel, Kenas son, Calebs yngsta broders; och han gaf honom sina dotter Achsa till hustru.
14 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
Och det begaf sig, då hon indrog, vardt henne rådet, att hon skulle bedas en åker af sin fader; och hon gaf sig ifrån åsnanom. Då sade Caleb till henne: Hvad är dig?
15 Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
Hon sade: Gif mig en välsignelse; ty du hafver gifvit mig ett söderland; gif mig ock ett, som vatten hafver. Då gaf han henne ett, som vatten hade ofvan och nedan.
16 Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
Och de Keniters barn, Mose svågers, drogo upp utu Palma staden med Juda barn uti Juda öken, som ligger sunnan för den staden Arad; och gingo till, och bodde ibland folket.
17 Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
Och Juda drog åstad med hans broder Simeon, och slogo de Cananeer i Zephat, och gåfvo honom tillspillo, och kallade staden Horma.
18 Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
Dertill vann Juda Gaza med dess tillhöring, och Askelon med dess tillhöring, och Ekron med dess tillhöring.
19 Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
Och Herren var med Juda, så att han intog berget; förty han kunde icke intaga dem som i dalarna bodde, derföre, att de hade jernvagnar.
20 Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
Och de gåfvo Caleb Hebron, såsom Mose sagt hade; och han fördref derut de tre Enaks söner.
21 Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
Men BenJamins barn fördrefvo icke de Jebuseer, som bodde i Jerusalem; utan de Jebuseer bodde när BenJamins barn i Jerusalem, allt intill denna dag.
22 To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
Sammalunda drogo ock Josephs barn upp till BethEl; och Herren var med dem.
23 Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
Och Josephs hus bespejade BethEl, det tillförene het Lus.
24 ’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
Och hållarena fingo se en man gå utu staden, och sade till honom: Visa oss huru vi skole komma in i staden, så vilje vi göra barmhertighet med dig.
25 Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
Och när han hade vist dem hvar de skulle komma in, slogo de staden med svärdsegg; men den mannen och all hans slägt läto de gå.
26 Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
Då drog den samme mannen in uti de Hetheers land, och byggde en stad, och kallade honom Lus. Den heter ännu i dag så.
27 Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
Och Manasse fördref icke BethSean med dess döttrar; icke heller Thaanach med dess döttrar, och icke heller de inbyggare i Dor med dess döttrar, ej heller de inbyggare i Jibleam med dess döttrar, ej heller de inbyggare i Megiddo med dess döttrar; och de Cananeer begynte till att bo i de samma landena.
28 Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
Men då Israel kom till magt, gjorde han de Cananeer skattpligtiga, och fördref dem icke.
29 Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
Sammalunda fördref icke heller Ephraim de Cananeer, som bodde i Gaser; utan de Cananeer bodde ibland dem i Gaser.
30 Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
Sebulon fördref icke heller dem som bodde i Kitron och Nahalol; utan de Cananeer bodde ibland dem, och voro skattpligtige.
31 Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
Asser fördref icke dem som bodde i Acco; icke heller dem som bodde i Zidon, i Ahlab, i Achsib, i Helbah, i Aphik och i Rehob;
32 kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
Utan de Asseriter bodde ibland de Cananeer, som i landena bodde; ty de fördrefvo dem icke.
33 Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
Napthali fördref icke dem som bodde i BethSemes, ej heller i BethAnath; utan bodde ibland de Cananeer, som i landena bodde; men de i BethSemes och i BethAnath vordo skattpligtige.
34 Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
Men de Amoreer trängde Dans barn in på bergena, och stadde dem icke till, att de kommo neder i dalarna.
35 Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
Och de Amoreer begynte bo på de bergena Heres i Ajalon och Saalbim; dock vardt Josephs hus hand dem för svår, så att de vordo skattpligtige.
36 Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.
Och de Amoreers gränsa var der man uppgår till Akrabbim, och ifrå klippone, och ifrå höjdene.

< Mahukunta 1 >