< Mahukunta 1 >

1 Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
Après la mort de Josué, les enfants d’Israël consultèrent le Seigneur, disant: Qui montera devant nous contre le Chananéen, et sera le chef de la guerre?
2 Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
Et le Seigneur répondit: Juda montera; voilà que j’ai livré la terre en ses mains.
3 Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
Alors Juda dit à Siméon, son frère: Monte avec moi dans mon lot; et combats contre le Chananéen, afin que moi-même j’aille dans ton lot. Et Siméon alla avec lui.
4 Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
Et Juda monta, et le Seigneur livra le Chananéen et le Phérézéen en leurs mains, et ils battirent à Bézec dix mille hommes.
5 A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
Ils trouvèrent ensuite Adonibézec à Bézec; ils combattirent contre lui, et défirent le Chananéen et le Phérézéen.
6 Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
Or, Adonibézec s’enfuit; l’ayant poursuivi, ils le prirent et coupèrent les extrémités de ses mains et de ses pieds.
7 Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
Et Adonibézec dit: Soixante-dix rois, les extrémités de leurs mains et de leurs pieds ayant été coupées, ramassaient sous ma table les restes des aliments: comme j’ai fait, ainsi Dieu m’a rétribué. Et ils l’emmenèrent à Jérusalem, et il y mourut.
8 Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
Or, les enfants de Juda ayant attaqué Jérusalem, la prirent et la frappèrent du tranchant du glaive, livrant aux flammes toute la ville.
9 Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
Et ensuite descendant, ils combattirent contre le Chananéen, qui habitait dans les montagnes, et vers le midi, et dans les plaines.
10 Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
Et Juda, marchant contre le Chananéen, qui habitait à Hébron (dont le nom fut anciennement Cariath-Arbé), battit Sésaï, Ahiman et Tholmaï.
11 Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
Puis, parti de là, il alla vers les habitants de Dabir, dont nom était Cariath-Sépher, c’est-à-dire Ville des lettres.
12 Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
Alors Caleb dit: Celui qui attaquera Cariath-Sépher, et la ravagera, je lui donnerai ma fille Axa pour femme.
13 Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
Or, comme Othoniel, fils de Cénez, et frère puîné de Caleb, la prit, il lui donna Axa, sa fille, pour femme.
14 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
Axa étant en chemin, son mari l’avertit de demander à son père le champ. Et comme elle soupirait, pendant qu’elle était montée sur l’âne, Caleb lui dit: Qu’as-tu?
15 Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
Et elle répondit: Accorde-moi une grâce; puisque c’est une terre aride que tu m’as donnée, donne-m’en aussi une arrosée par des eaux. Caleb donc lui en donna une arrosée par le haut et arrosée par le bas,
16 Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
Or, les enfants d’un Cinéen, parent de Moïse, montèrent de la Ville des palmes, avec les enfants de Juda, au désert de leur lot, lequel est vers le midi d’Arad, et habitèrent avec eux.
17 Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
Cependant Juda s’en alla avec Siméon, son frère; ils attaquèrent ensemble le Chananéen qui habitait à Séphaath, et ils le tuèrent. Et la ville fut appelée du nom d’Horma, c’est-à-dire anathème.
18 Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
Juda prit aussi Gaza avec ses confins, Ascalon et Accaron avec leurs frontières.
19 Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
Et le Seigneur fut avec Juda, et Juda posséda les montagnes; mais il ne put détruire les habitants de la vallée, parce qu’ils avaient une grande quantité de chars armés de faux.
20 Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
Et ils donnèrent, comme Moïse avait dit, Hébron à Caleb, qui en extermina les trois fils d’Enac.
21 Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
Mais les enfants de Benjamin ne détruisirent pas le Jébuséen, habitant de Jérusalem; ainsi, le Jébuséen a habité avec les enfants de Benjamin à Jérusalem, jusqu’au présent jour.
22 To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
La maison de Joseph aussi monta vers Béthel; et le Seigneur fut avec eux.
23 Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
Car, comme ils assiégeaient la ville, qui auparavant était appelée Luza,
24 ’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
Ils virent un homme sortant de la cité, et ils lui dirent: Montre-nous l’entrée de la ville, et nous te ferons miséricorde.
25 Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
Lorsque cet homme la leur eut montrée, ils frappèrent la ville du tranchant du glaive; mais cet homme et toute sa parenté, ils les renvoyèrent.
26 Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
Cet homme renvoyé, s’en alla dans la terre d’Hetthim, et il bâtit là une ville et l’appela Luza, laquelle est ainsi appelée jusqu’au présent jour.
27 Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
Manassé aussi ne détruisit pas Bethsan et Thanac avec leurs bourgades, ni les habitants de Dor, ni Jéblaam, ni Mageddo avec ses bourgades; et le Chananéen commença à habiter avec eux.
28 Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
Mais lorsqu’Israël se fut fortifié, il les rendit tributaires, et il ne voulut pas les détruire.
29 Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
Ephraïm de même ne tua pas le Chananéen, qui habitait à Gazer, mais le Chananéen habita avec lui.
30 Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
Zabulon ne détruisit pas les habitants de Cétron et de Naalol; mais le Chananéen habita au milieu de lui et lui devint tributaire.
31 Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
Azer aussi ne détruisit pas les habitants d’Accho et de Sidon, ni Ahalab, ni Achazib, ni Helba, ni Aphec, ni Rohob;
32 kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
Mais il habita au milieu du Chananéen, habitant de cette terre, et il ne le tua pas.
33 Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
Nephthali aussi ne détruisit pas les habitants de Bethsamès, et de Béthanath; mais il habita parmi le Chananéen habitant de cette terre; et les Bethsamites, et les Béthanites lui furent tributaires.
34 Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
L’Amorrhéen resserra les enfants de Dan sur la montagne, et il ne leur donna pas lieu de s’étendre dans la plaine;
35 Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
Et il habita sur la montagne d’Harès, que l’on interprète montagne de têts, dans Aïalon et Salébim. Et la puissance de la maison de Joseph s’accrut, et l’Amorrhéen lui devint tributaire.
36 Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.
Or, la frontière de l’Amorrhéen fut depuis la montée du Scorpion, le rocher et les lieux plus élevés.

< Mahukunta 1 >