< Mahukunta 1 >
1 Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
Après la mort de Josué, les enfants d’Israël consultèrent le Seigneur en disant: "Qui de nous doit marcher le premier contre le Cananéen pour l’attaquer?"
2 Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
Le Seigneur répondit: "C’Est Juda qui doit marcher; je livre le pays en son pouvoir."
3 Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
Alors Juda dit à Siméon, son frère: "Aide-moi à faire la guerre au Cananéen dans mon territoire et à mon tour je ferai campagne avec toi dans le tien." Et Siméon se joignit à lui.
4 Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
Juda se mit en marche, et le Seigneur livra le Cananéen et le Phérézéen en son pouvoir; ils les défirent à Bézek, au nombre de dix mille hommes.
5 A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
Ils trouvèrent Adoni-Bézek à Bézek, l’attaquèrent, et achevèrent de battre le Cananéen et le Phérézéen.
6 Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
Adoni-Bézek ayant pris la fuite, ils le poursuivirent, le prirent et lui coupèrent les pouces et les orteils.
7 Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
Et Adoni-Bézek dit: "Soixante-dix rois, ayant les pouces et les orteils coupés, ont ramassé les miettes sous ma table; ce que j’ai fait, Dieu me le rend!" On le conduisit à Jérusalem, et il y mourut.
8 Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
Les enfants de Juda attaquèrent Jérusalem, s’en emparèrent, passèrent la population au fil de l’épée, et livrèrent la ville aux flammes.
9 Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
Après quoi, les enfants de Juda descendirent attaquer les Cananéens qui habitaient la montagne, ceux du Midi et de la plaine.
10 Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
Puis Juda marcha contre les Cananéens qui habitaient Hébron Hébron portait autrefois le nom de Cité d’Arba et ils battirent Chêchaï, Ahimân et Talmaï.
11 Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
De là on se dirigea vers les habitants de Debir, laquelle s’appelait autrefois Kiryat-Sêfer.
12 Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
Et Caleb dit: "Celui qui triomphera de Kiryat-Sêfer et la prendra, je lui donnerai ma fille Akhsa pour épouse."
13 Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
Elle fut prise par Othoniel, fils de Kenaz, frère puîné de Caleb, et celui-ci lui donna pour femme sa fille Akhsa.
14 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
En se rendant près de son époux, elle l’incita à demander le domaine à son père; puis elle-même descendit de l’âne, et Caleb lui ayant demandé: "Que veux-tu?"
15 Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
Elle lui répondit: "Fais-moi un présent, car tu m’as reléguée dans un pays aride; donne-moi donc des sources d’eau! Et Caleb lui donna les sources du pays haut et celles du pays bas.
16 Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
Les descendants de Kéni, beau-père de Moïse, montèrent avec ceux de Juda de la ville des Palmiers au désert de Juda, qui est au midi d’Arad; et ils s’y établirent parmi le peuple.
17 Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
Juda se mit encore en campagne avec Siméon, son frère, et ils battirent le Cananéen habitant Cefat; ils vouèrent la ville à l’anathème, et elle reçut le nom de Horma.
18 Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
Puis Juda prit Gaza avec son territoire, Ascalon avec le sien, Ekron avec le sien.
19 Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
Le Seigneur fut avec Juda, de sorte qu’il put conquérir la montagne; mais il ne put déposséder les habitants de la vallée, qui avaient des chariots armés de fer.
20 Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
Caleb eut pour apanage Hébron, comme l’avait dit Moïse, et il en expulsa les trois fils d’Anak.
21 Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
Pour les Jébuséens, habitants de Jérusalem, les enfants de Benjamin ne les dépossédèrent point, et ils sont restés à Jérusalem, avec les enfants de Benjamin, jusqu’à ce jour.
22 To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
De leur côté, les descendants de Joseph marchèrent sur Béthel, et le Seigneur fut avec eux.
23 Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
Ils firent explorer les abords de Béthel, ville qui autrefois avait nom Louz.
24 ’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
Or, les soldats de garde, voyant un homme qui sortait de la ville, lui dirent: "Montre-nous par où l’on peut entrer dans la ville, et nous te traiterons avec faveur."
25 Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
Il leur indiqua le moyen de pénétrer dans la ville, et ils passèrent les habitants au fil de l’épée, mais laissèrent partir l’homme avec toute sa famille.
26 Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
Celui-ci se retira au pays des Héthéens; il bâtit une ville qu’il nomma Louz, et ce nom lui est resté jusqu’aujourd’hui.
27 Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
Pour Manassé, il ne déposséda point les gens de Beth-Cheân et de ses dépendances, ceux de Taanakh et de ses dépendances, ni les habitants de Dor et de ses dépendances, ni ceux de Yibleâm avec les siennes, ni ceux de Meghiddo avec les siennes, le Cananéen persistant à demeurer dans ce pays.
28 Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
Devenu plus puissant, Israël soumit le Cananéen à un tribut, mais il ne l’expulsa point.
29 Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
Ephraïm non plus n’expulsa le Cananéen établi à Ghézer, de sorte que le Cananéen demeura côte à côte avec lui à Ghézer.
30 Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
Zabulon n’expulsa point les habitants de Kitrôn ni ceux de Nahalol; ces Cananéens demeurèrent avec lui, mais payèrent tribut.
31 Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
Aser n’expulsa point les habitants d’Acco ni ceux de Sidon, d’Ahlab, d’Akhzib, de Helba, d’Afik et de Rehob.
32 kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
Les Asérites demeurèrent donc au milieu des Cananéens qui occupaient ce pays, ne les ayant point dépossédés.
33 Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
Nephtali n’expulsa pas les habitants de Beth-Chémech, ni ceux de Beth-Anat, et il demeura au milieu des Cananéens qui habitaient ce pays; mais les habitants de Beth-Chémech et de Beth-Anat leur payèrent tribut.
34 Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
Les Amorréens refoulèrent les enfants de Dan sur la montagne, en ne les laissant pas descendre dans la vallée.
35 Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
Ces Amorréens voulurent rester à Har-Hérès, à Ayyalôn et à Chaalbîm; mais, dominés par la puissance supérieure de la maison de Joseph, ils devinrent tributaires.
36 Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.
Le territoire des Amorréens commençait à la montée d’Akrabbîm, à partir de Séla et au-dessus.