< Mahukunta 9 >

1 Abimelek ɗan Yerub-Ba’al ya tafi Shekem wurin’yan’uwan mahaifiyarsa, ya ce musu da kuma dukan dangin mahaifiyarsa,
Jerubáalov sin Abiméleh je šel do Sihema, do bratov svoje matere in se z njimi posvetoval in z vso družino hiše očeta svoje matere, rekoč:
2 “Ku tambayi’yan ƙasar Shekem, ‘Wanne ya fi muku, a sa dukan’ya’yan Yerub-Ba’al saba’in maza su yi mulkinku, ko dai mutum guda kawai yă yi mulkinku?’ Ku tuna, ni jininku ne.”
»Govorite, prosim vas, na ušesa vsem sihemskim gospodarjem: ›Ali je za vas bolje, da vsi Jerubáalovi sinovi, katerih je sedemdeset oseb, kraljujejo nad vami ali da nad vami kraljuje eden? Spomnite se tudi, da sem jaz vaša kost in vaše meso.‹«
3 Sa’ad da’yan’uwan suka mayar wa’yan ƙasar Shekem wannan, sai suka goyi bayan Abimelek, gama sun ce, “Shi ɗan’uwanmu ne.”
Bratje njegove matere so vse te besede o njem govorili v ušesa vseh sihemskih gospodarjev in njihova srca nagnili, da sledijo Abimélehu, kajti rekli so: »On je naš brat.«
4 Suka ba shi shekel saba’in na azurfa daga haikalin Ba’al-Berit, Abimelek kuwa ya yi amfani da shi ya yi hayar’yan tauri waɗanda suka zama masu binsa.
Iz hiše Baal-berita so mu dali sedemdeset koščkov srebra, s katerimi je Abiméleh najel prazno-glave in nepomembne osebe, ki so mu sledili.
5 Sai ya tafi gidan mahaifinsa a Ofra kuma a dutse guda ya kashe’yan’uwansa,’ya’yan Yerub-Ba’al. Amma Yotam, autan ɗan Yerub-Ba’al ya tsira ta wurin ɓuya.
Odšel je v hišo svojega očeta pri Ofri in na enem kamnu usmrtil svoje brate, Jerubáalove sinove, ki jih je bilo sedemdeset oseb. Kljub temu pa je ostal najmlajši Jerubáalov sin Jotám, kajti ta se je skril.
6 Sa’an nan duka’yan ƙasar Shekem da Bet Millo suka taru kusa da babban itacen wajen ginshiƙi a Shekem don a naɗa Abimelek sarki.
Vsi sihemski gospodarji so se zbrali skupaj in vsa Milójeva hiša in odšli ter Abiméleha postavili za kralja pri ravninskem stebru, ki je bil v Sihemu.
7 Sa’ad da aka gaya wa Yotam wannan, sai ya hau Dutsen Gerizim ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku saurare ni,’yan ƙasar Shekem, don Allah yă saurare ku.
Ko so to povedali Jotámu, je ta odšel in se postavil na vrhu gore Garizím, povzdignil svoj glas, zavpil in jim rekel: »Prisluhnite mi, vi sihemski gospodarji, da bo Bog lahko prisluhnil vam.
8 Wata rana itatuwa suka fita don su naɗa wa kansu sarki. Suka ce wa itacen zaitun, ‘Ka zama sarkinmu.’
Drevesa so šla naprej ob času, da mazilijo kralja nad seboj in rekla so oljki: ›Kraljuj nad nami.‹
9 “Amma itacen zaitun ya ce, ‘In bar mai nawa, wanda da shi ake girmama alloli da mutane, don in zo in yi ta fama da itatuwa?’
Toda oljka jim je rekla: ›Mar naj zapustim svojo mastnost, s katero po meni častijo Boga in človeka in grem, da bi bila povišana nad drevesa?‹
10 “Biye da wannan, sai itatuwan suka ce wa itacen ɓaure, ‘Zo ka zama sarkinmu.’
Drevesa so rekla figovemu drevesu: ›Ti pridi in kraljuj nad nami.‹
11 “Amma itacen ɓauren ya ce, ‘In bar kyawawan’ya’yana da zaƙinsu, in zo in yi ta fama da itatuwa?’
Toda figovo drevo jim je reklo: ›Mar naj zapustim svojo sladkost in svoj dober sad in grem, da bi bilo povišano nad drevesa?‹
12 “Sa’an nan itatuwan suka ce wa kuringar inabi, ‘Ki zo ki zama sarkinmu.’
Potem so drevesa rekla trti: ›Ti pridi in kraljuj nad nami.‹
13 “Amma kuringar ta ce, ‘In bar ruwan inabina, wanda yake faranta zuciyar alloli da mutane, in zo in yi fama da itatuwa?’
Trta pa jim je rekla: ›Mar naj zapustim svoje vino, ki razveseljuje Boga in človeka in grem, da naj bi bila povišana nad drevesa?‹
14 “A ƙarshe sai dukan itatuwa suka ce wa itacen ƙaya, ‘Ka zo ka zama sarkinmu.’
Potem so vsa drevesa rekla trnovemu grmu: ›Ti pridi in kraljuj nad nami.‹
15 “Itacen ƙaya ya ce wa itatuwan, ‘In da gaske ne kuke so ku naɗa ni sarkinku, ku zo ku sha inuwana; in ba haka ba, bari wuta ta fito daga itacen ƙaya ta cinye itacen al’ul na Lebanon!’
Trnov grm je rekel drevesom: ›Če me resnično mazilite za kralja nad seboj, potem pridite in svoje zaupanje položite v mojo senco, in če ne, naj ogenj pride iz trnovega grma in použije libanonske cedre.‹
16 “To, da a ce kun yi abin bangirma da aniya mai kyau sa’ad da kuka naɗa Abimelek sarki, da kun nuna wa Yerub-Ba’al da iyalinsa ladabi, da kuma kun yi masa abin da ya cancanci shi,
Zdaj torej, če ste storili resnično in iskreno v tem, da ste si postavili Abiméleha za kralja in če ste dobro postopali z Jerubáalom in njegovo hišo in mu storili glede na ravnanje njegovih rok
17 a yi tunani cewa mahaifina ya yi yaƙi saboda ku, ya yi kasai da ransa don yă cece ku daga hannun Midiyawa
(kajti moj oče se je bojeval za vas in v ospredju tvegal svoje življenje in vas osvobodil iz roke Midjáncev
18 (amma ga shi yau kun tayar wa iyalin mahaifina, kuka kashe’ya’yansa saba’in a dutse guda, kuka kuma naɗa Abimelek, ɗan baiwa, sarki a kan’yan ƙasar Shekem domin shi ɗan’uwanku ne)
in ste ta dan vstali zoper hišo mojega očeta in umorili njegove sinove, sedemdeset oseb na enem kamnu in postavili Abiméleha, sina njegove dekle, za kralja nad sihemskimi gospodarji, ker je vaš brat).
19 in har kun aikata wannan cikin bangirma da kuma aminci wajen Yerub-Ba’al da iyalinsa a yau, bari Abimelek yă zama farin cikinku, ku kuma nasa!
Če ste torej ta dan resnično in iskreno postopali z Jerubáalom in njegovo hišo, potem se veselite z Abimélehom in naj se tudi on veseli z vami.
20 Amma in ba haka ba, bari wuta ta fito daga Abimelek ya cinye ku,’yan ƙasar Shekem da Bet Millo, bari wuta kuma daga wurinku’yan ƙasar Shekem da Bet Millo ta cinye Abimelek!”
Toda če ne, naj ogenj pride od Abiméleha in pogoltne sihemske gospodarje in Milójevo hišo. In ogenj naj pride od sihemskih gospodarjev in od Milójeve hiše in požre Abiméleha.
21 Sa’an nan Yotam ya gudu, ya tsere zuwa Beyer ya zauna a can gama yana tsoron ɗan’uwansa Abimelek.
Jotám je stekel proč, pobegnil in odšel v Beêr in tam prebival zaradi strahu pred svojim bratom Abimélehom.
22 Bayan Abimelek ya yi shekara uku yana mulki a Isra’ila,
Ko je Abiméleh tri leta kraljeval nad Izraelom,
23 sai Allah ya aiko da mugun ruhu tsakanin Abimelek da’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka ci amanar Abimelek.
je potem Bog med Abiméleha in sihemske gospodarje poslal zlega duha in sihemski gospodarji so zahrbtno postopali z Abimélehom,
24 Allah ya yi haka saboda kisan’ya’ya saba’in na Yerub-Ba’al, don a ɗauki fansar jininsu a kan Abimelek ɗan’uwansu da kuma’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka taimake shi kisan’yan’uwansa.
da bi ta krutost, storjena sedemdesetim Jerubáalovim sinovom lahko prišla in bi bila njihova kri položena na njihovega brata Abiméleha, ki jih je umoril in na sihemske gospodarje, ki so mu pomagali pri morjenju njegovih bratov.
25 Cikin hamayya da shi waɗannan’yan ƙasar Shekem suka sa mutane a kan tuddai don su yi kwanton ɓauna a kan su yi fashi ga duk wanda ya wuce a can, wannan fa ya kai kunnen Abimelek.
Sihemski gospodarji so zanj postavili prežavce v zasedi na vrhu gora in ti so oropali vse, ki so mimo njih prišli po tej poti, in to je bilo povedano Abimélehu.
26 To, Ga’al ɗan Ebed ya tafi tare da’yan’uwansa zuwa Shekem,’yan ƙasarta kuwa suka dogara da shi.
Ebedov sin Gáal je prišel s svojimi brati in odšel preko v Sihem in sihemski gospodarji so svoje zaupanje položili vanj.
27 Bayan sun tafi gonaki suka tattara inabi suka matse su, sai suka yi biki a haikalin allahnsu. Yayinda suke ci da sha, sai suka la’anci Abimelek.
Odšli so ven na polja in obrali svoje vinograde in tlačili grozdje in se veselili in odšli v hišo svojega boga, jedli, pili in preklinjali Abiméleha.
28 Sa’an nan Ga’al ɗan Ebed ya ce, “Wane ne Abimelek, kuma wane ne Shekem, da za mu bauta masa? Shi ba ɗan Yerub-Ba’al ba ne, kuma ba Zebul ne mataimakinsa ba? Ku bauta wa mutanen Hamor, mahaifin Shekem! Me ya sa za mu bauta wa Abimelek?
Ebedov sin Gáal je rekel: »Kdo je Abiméleh in kdo je Sihem, da bi mu služili? Mar ni on Jerubáalov sin? In Zebúl njegov častnik? Služite možem Sihemovega očeta Hamórja, kajti zakaj bi mi služili njemu?
29 Da a ce waɗannan mutane suna a ƙarƙashina mana! Da zan hamɓarar da shi. In ce wa Abimelek, ‘Ka tara dukan mayaƙanka!’”
Bog daj, da bi bilo to ljudstvo pod mojo roko! Potem bi odstranil Abiméleha.« In Abimélehu je rekel: »Okrepi svojo vojsko in pridi ven.«
30 Sa’ad da Zebul gwamnar birnin ya ji abin da Ga’al ɗan Ebed ya ce, sai ya fusata.
Ko je Zebúl, vladar mesta, slišal besede Ebedovega sina Gáala, je bila njegova jeza vžgana.
31 Asirce sai ya aiki manzanni wajen Abimelek, yana cewa, “Ga’al ɗan Ebed da’yan’uwansa sun zo Shekem suna kuma zuga birnin sun tayar maka.
Na skrivnem je poslal poslance k Abimélehu, rekoč: »Glej, Ebedov sin Gáal in njegovi bratje so prišli v Sihem in glej, zoper tebe utrjujejo mesto.
32 To, in dare ya yi, sai ka zo da mutanenka ku yi kwanto a filaye.
Zdaj se torej dvigni ponoči ti in ljudstvo, ki je s teboj in na polju prežite v zasedi
33 Kashegari da safe, sai ku tashi ku fāɗa wa birnin. Sa’ad da Ga’al da mutanensa suka faɗa maka, sai ka yi abin da ka iya yi da su.”
in zgodilo se bo, da zjutraj, takoj ko bo sonce vzšlo, da boš zgodaj vstal in se nameril na mesto. In glej, ko bodo on in ljudstvo, ki je z njim, prišli ven zoper tebe, potem jim boš lahko storil kakor boš našel priložnost.«
34 Saboda haka Abimelek da dukan mutanensa suka tashi da dare suka ɓuya kusa da Shekem a ƙungiyoyi huɗu.
Abiméleh je ponoči vstal in vse ljudstvo, ki je bilo z njim in so v štirih skupinah prežali zoper Sihem.
35 To, Ga’al ɗan Ebed ya riga ya fita waje yana tsaye a ƙofar birni daidai Abimelek da mayaƙansa suka fito daga inda suka ɓuya.
Ebedov sin Gáal je odšel ven in stal v vhodu velikih vrat mesta. Abiméleh in ljudstvo, ki je bilo z njim, pa je vstalo od prežanja.
36 Sa’ad da Ga’al ya gan su, sai ya ce wa Zebul, “Duba, ga mutane suna gangarowa daga kan duwatsu!” Zebul ya ce, “Kana ɗaukan inuwan duwatsu kana ce mutane.”
Ko je Gáal zagledal ljudstvo, je rekel Zebúlu: »Glej, tam prihaja ljudstvo dol iz vrha gorovja.« Zebúl mu je rekel: »Senco gorovja vidiš, kakor bi bili možje.«
37 Amma Ga’al ya sāke magana ya ce, “Duba, mutane suna gangarowa daga tsakiyar filaye, kuma wata ƙungiya tana zuwa daga wajen itacen masu duba.”
Gáal je ponovno spregovoril in rekel: »Vidiš, tam prihaja dol ljudstvo po sredi dežele in druga skupina prihaja vzdolž ravnine Maonim.«
38 Sa’an nan Zebul ya ce masa, “Ina bakin da ka yi ɗin, kai da ka ce, ‘Wane ne Abimelek da za mu bauta masa.’ Ba mutanen ne ka yi musu ba’a ba? Fita, ka yaƙe su mana!”
Potem mu je Zebúl rekel: »Kje so sedaj tvoja usta, s katerimi praviš: ›Kdo je Abiméleh, da bi mu služili?‹ Mar ni to ljudstvo, ki si ga preziral? Pojdi sedaj ven, prosim te in se bori z njimi.«
39 Saboda haka Ga’al ya fito da’yan ƙasar Shekem suka yaƙi Abimelek.
Gáal je odšel ven pred sihemskimi gospodarji in se boril z Abimélehom.
40 Abimelek ya kore shi, mutane da yawa suka ji ciwo a yaƙin, har zuwa ƙofar birnin.
Abiméleh ga je pregnal in ta je pobegnil pred njim in mnogi so bili zrušeni in ranjeni, celó do vhoda velikih vrat.
41 Abimelek ya zauna a Aruma, Zebul kuwa ya kori Ga’al da’yan’uwansa daga Shekem.
Abiméleh je prebival pri Arúmi, Zebúl pa je vrgel ven Gáala in njegove brate, da ne bi prebivali v Sihemu.
42 Kashegari mutanen Shekem suka tafi gonaki, aka kuwa gaya wa Abimelek.
Naslednji dan se je pripetilo, da je ljudstvo odšlo ven na polje in povedali so Abimélehu.
43 Saboda haka ya ɗauki mutanensa, ya raba su ƙungiya uku, sa’an nan ya yi kwanto a gonakin. Sa’ad da ya ga mutanen suna fitowa daga birni, sai ya yi wuf ya fāɗa musu.
Ta je vzel ljudstvo in jih razdelil v tri skupine. Na polju so prežali v zasedi in glej, ljudstvo je prišlo ven iz mesta. Vstal je zoper njih in jih udaril.
44 Abimelek da ƙungiyoyin da suke tare da shi suka yi maza suka yi tsaya a ƙofar birnin. Sa’an nan ƙungiyoyi biyu suka ruga suka fāɗa wa waɗanda suke a gonaki suka karkashe su.
Abiméleh in skupina, ki je bila z njim, je pohitela naprej in stala na vhodu velikih vrat mesta in dve drugi skupini sta stekli nad vse ljudstvo, ki je bilo na poljih in jih usmrtili.
45 Dukan yinin, Abimelek ya matsa yaƙi da birnin sai da ya cinye ta ya kuma kashe mutanenta. Sa’an nan ya hallaka birnin ya barbaza gishiri a kanta.
Abiméleh se je ves tisti dan boril zoper mesto, zavzel mesto, usmrtil ljudstvo, ki je bilo v njem, premagal mesto in ga potresel s soljo.
46 Da jin haka, sai’yan ƙasa a hasumiyar Shekem suka shiga wurin mafaka a hankalin El-Berit.
Ko so vsi gospodarji sihemskega stolpa to slišali, so vstopili v trdnjavo hiše boga Berita.
47 Da Abimelek ya ji dukan mutanen hasumiyar Shekem sun taru a can,
To je bilo povedano Abimélehu, da so bili vsi gospodarji sihemskega stolpa zbrani skupaj.
48 sai Abimelek da dukan mutanensa suka haura zuwa Dutsen Zalmon. Sai ya ɗauki gatari ya sassare waɗansu rassa, waɗanda ya sa a kafaɗunsa. Ya umarci mutanen da suke tare da shi ya ce, “Sauri, ku yi abin da kuka ga na yi!”
Abiméleh se je povzpel na goro Calmón, on in vse ljudstvo, ki je bilo z njim in Abiméleh je v svojo roko vzel sekiro, odsekal vejo iz dreves, jo vzel in jo položil na svojo ramo in rekel ljudstvu, ki je bilo z njim: »Kar ste videli storiti mene, pohitite in storite, kakor sem storil jaz.«
49 Saboda haka mutanen suka sassare rassan itatuwa suka bi Abimelek. Suka tattara su a jikin mafakar suka kuma cinna mata wuta a kan mutanen da suke a ciki. Ta haka dukan mutanen da suke cikin hasumiyar Shekem, wajen maza da mata dubu ɗaya suka mutu.
Podobno je vse ljudstvo odsekalo vsak svojo vejo, sledilo Abimélehu, jih položili k trdnjavi in zažgali trdnjavo nad njimi. Tako da so umrli tudi vsi ljudje iz sihemskega stolpa, okoli tisoč mož in žena.
50 Biye da wannan Abimelek ya tafi Tebez, ya kewaye ta ya kuma cinye ta da yaƙi.
Potem je Abiméleh odšel v Tebéc, se utaboril zoper Tebéc in ga zavzel.
51 A cikin birnin, akwai wata hasumiya mai ƙarfi, inda dukan maza da mata, dukan mutanen birnin, suka ɓuya. Suka kulle kansu, suka kuma hau rufin hasumiyar.
Toda tam, znotraj mesta, je bil močan stolp in tja so pobegnili vsi možje in žene in vsi iz mesta in ga za seboj zaprli in se spravili na vrh stolpa.
52 Abimelek ya je wajen hasumiya ya kuma auka mata. Amma da ya yi kusa da ƙofar hasumiyar don yă cinna mata wuta,
Abiméleh je prišel k stolpu, se boril zoper njega in se približal vratom stolpa, da bi ga zažgal z ognjem.
53 sai wata mata ta saki ɗan dutsen niƙa a kan Abimelek ta fasa ƙoƙon kansa.
Neka ženska je kos mlinskega kamna vrgla na Abimélehovo glavo in razbila njegovo lobanjo.
54 Da sauri ya kira mai riƙon masa makami ya ce, “Zaro takobinka ka kashe ni, don kada a ce ‘Mace ce ta kashe shi.’” Saboda haka bawansa ya soke shi, ya mutu.
Potem je naglo zaklical k mladeniču, svojemu nosilcu bojne opreme in mu rekel: »Izvleci svoj meč in me usmrti, da ne bodo ljudje o meni rekli: ›Ubila ga je ženska.‹« In njegov mladenič ga je prebodel in ta je umrl.
55 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga Abimelek ya mutu, sai suka tafi gida.
Ko so možje iz Izraela videli, da je bil Abiméleh mrtev, so odšli vsak mož na svoj kraj.
56 Ta haka Allah ya sāka muguntar da Abimelek da ya yi wa mahaifinsa ta wurin kisan’yan’uwansa saba’in.
Tako je Bog povrnil Abimélehovo zlobnost, ki jo je storil svojemu očetu z umorom svojih sedemdesetih bratov
57 Allah kuma ya sa muguntar mutanen Shekem suka koma kansu. La’anar Yotam ɗan Yerub-Ba’al kuma ta kama su.
in vse zlo sihemskih ljudi je Bog povrnil na njihove glave in nadnje je prišlo prekletstvo Jerubáalovega sina Jotáma.

< Mahukunta 9 >