< Mahukunta 9 >

1 Abimelek ɗan Yerub-Ba’al ya tafi Shekem wurin’yan’uwan mahaifiyarsa, ya ce musu da kuma dukan dangin mahaifiyarsa,
Abimélec, fils de Jerubbaal, se rendit à Sichem, chez les frères de sa mère, et leur parla, ainsi qu'à toute la famille de la maison du père de sa mère, en disant:
2 “Ku tambayi’yan ƙasar Shekem, ‘Wanne ya fi muku, a sa dukan’ya’yan Yerub-Ba’al saba’in maza su yi mulkinku, ko dai mutum guda kawai yă yi mulkinku?’ Ku tuna, ni jininku ne.”
« Parle, je te prie, aux oreilles de tous les hommes de Sichem: « Vaut-il mieux pour vous que tous les fils de Jerubbaal, qui sont soixante-dix personnes, dominent sur vous, ou qu'un seul domine sur vous? ». Souvenez-vous aussi que je suis votre os et votre chair. »
3 Sa’ad da’yan’uwan suka mayar wa’yan ƙasar Shekem wannan, sai suka goyi bayan Abimelek, gama sun ce, “Shi ɗan’uwanmu ne.”
Les frères de sa mère rapportèrent de lui toutes ces paroles aux oreilles de tous les hommes de Sichem. Leur cœur penchait pour suivre Abimélec, car ils disaient: « C'est notre frère. »
4 Suka ba shi shekel saba’in na azurfa daga haikalin Ba’al-Berit, Abimelek kuwa ya yi amfani da shi ya yi hayar’yan tauri waɗanda suka zama masu binsa.
Ils lui donnèrent soixante-dix pièces d'argent provenant de la maison de Baal Berith, avec laquelle Abimélec engageait des hommes vains et imprudents qui le suivaient.
5 Sai ya tafi gidan mahaifinsa a Ofra kuma a dutse guda ya kashe’yan’uwansa,’ya’yan Yerub-Ba’al. Amma Yotam, autan ɗan Yerub-Ba’al ya tsira ta wurin ɓuya.
Il se rendit à la maison de son père, à Ophra, et tua ses frères, les fils de Jerubbaal, soit soixante-dix personnes, sur une seule pierre; mais il resta Jotham, le plus jeune des fils de Jerubbaal, car il se cacha.
6 Sa’an nan duka’yan ƙasar Shekem da Bet Millo suka taru kusa da babban itacen wajen ginshiƙi a Shekem don a naɗa Abimelek sarki.
Tous les hommes de Sichem se rassemblèrent avec toute la maison de Millo, et ils allèrent établir roi Abimélec près du chêne de la colonne qui était à Sichem.
7 Sa’ad da aka gaya wa Yotam wannan, sai ya hau Dutsen Gerizim ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku saurare ni,’yan ƙasar Shekem, don Allah yă saurare ku.
Lorsqu'ils racontèrent cela à Jotham, celui-ci alla se placer sur le sommet du mont Garizim, éleva la voix, cria et leur dit: « Ecoutez-moi, hommes de Sichem, afin que Dieu vous écoute.
8 Wata rana itatuwa suka fita don su naɗa wa kansu sarki. Suka ce wa itacen zaitun, ‘Ka zama sarkinmu.’
Les arbres se mirent à oindre un roi sur eux. Ils dirent à l'olivier: « Règne sur nous ».
9 “Amma itacen zaitun ya ce, ‘In bar mai nawa, wanda da shi ake girmama alloli da mutane, don in zo in yi ta fama da itatuwa?’
« Mais l'olivier leur dit: « Dois-je cesser de produire mon huile, avec laquelle on honore Dieu et les hommes par moi, et aller m'agiter de long en large sur les arbres? ».
10 “Biye da wannan, sai itatuwan suka ce wa itacen ɓaure, ‘Zo ka zama sarkinmu.’
« Les arbres dirent au figuier: « Viens et règne sur nous ».
11 “Amma itacen ɓauren ya ce, ‘In bar kyawawan’ya’yana da zaƙinsu, in zo in yi ta fama da itatuwa?’
« Mais le figuier leur dit: « Dois-je laisser ma douceur et mon bon fruit, et aller m'agiter sur les arbres? ».
12 “Sa’an nan itatuwan suka ce wa kuringar inabi, ‘Ki zo ki zama sarkinmu.’
« Les arbres dirent à la vigne: « Viens et règne sur nous ».
13 “Amma kuringar ta ce, ‘In bar ruwan inabina, wanda yake faranta zuciyar alloli da mutane, in zo in yi fama da itatuwa?’
« La vigne leur dit: « Dois-je laisser mon vin nouveau, qui réjouit Dieu et les hommes, et aller m'agiter sur les arbres? ».
14 “A ƙarshe sai dukan itatuwa suka ce wa itacen ƙaya, ‘Ka zo ka zama sarkinmu.’
« Alors tous les arbres dirent à la ronce: « Viens et règne sur nous ».
15 “Itacen ƙaya ya ce wa itatuwan, ‘In da gaske ne kuke so ku naɗa ni sarkinku, ku zo ku sha inuwana; in ba haka ba, bari wuta ta fito daga itacen ƙaya ta cinye itacen al’ul na Lebanon!’
« La ronce dit aux arbres: 'Si vous m'oignez vraiment comme roi, venez vous réfugier à mon ombre; sinon, que le feu sorte de la ronce et dévore les cèdres du Liban'.
16 “To, da a ce kun yi abin bangirma da aniya mai kyau sa’ad da kuka naɗa Abimelek sarki, da kun nuna wa Yerub-Ba’al da iyalinsa ladabi, da kuma kun yi masa abin da ya cancanci shi,
« Maintenant, si vous avez agi avec vérité et droiture, en faisant régner Abimélec, et si vous avez bien traité Jerubbaal et sa maison, et si vous l'avez traité selon le mérite de ses mains
17 a yi tunani cewa mahaifina ya yi yaƙi saboda ku, ya yi kasai da ransa don yă cece ku daga hannun Midiyawa
(car mon père a combattu pour vous, a risqué sa vie, et vous a délivrés de la main de Madian;
18 (amma ga shi yau kun tayar wa iyalin mahaifina, kuka kashe’ya’yansa saba’in a dutse guda, kuka kuma naɗa Abimelek, ɗan baiwa, sarki a kan’yan ƙasar Shekem domin shi ɗan’uwanku ne)
et aujourd'hui, vous vous êtes levés contre la maison de mon père, vous avez tué ses fils, soixante-dix personnes, sur une seule pierre, et vous avez fait d'Abimélec, fils de sa servante, le roi des hommes de Sichem, parce qu'il est votre frère);
19 in har kun aikata wannan cikin bangirma da kuma aminci wajen Yerub-Ba’al da iyalinsa a yau, bari Abimelek yă zama farin cikinku, ku kuma nasa!
Si donc tu as traité aujourd'hui Jerubbaal et sa maison avec fidélité et justice, réjouis-toi en Abimélec, et que lui aussi se réjouisse en toi;
20 Amma in ba haka ba, bari wuta ta fito daga Abimelek ya cinye ku,’yan ƙasar Shekem da Bet Millo, bari wuta kuma daga wurinku’yan ƙasar Shekem da Bet Millo ta cinye Abimelek!”
sinon, que le feu sorte d'Abimélec et dévore les hommes de Sichem et de la maison de Millo; et que le feu sorte des hommes de Sichem et de la maison de Millo et dévore Abimélec. »
21 Sa’an nan Yotam ya gudu, ya tsere zuwa Beyer ya zauna a can gama yana tsoron ɗan’uwansa Abimelek.
Jotham s'est enfui et a fui, il est allé à Beer et y a vécu, par crainte d'Abimélec, son frère.
22 Bayan Abimelek ya yi shekara uku yana mulki a Isra’ila,
Abimélec fut prince sur Israël pendant trois ans.
23 sai Allah ya aiko da mugun ruhu tsakanin Abimelek da’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka ci amanar Abimelek.
Alors Dieu envoya un mauvais esprit entre Abimélec et les hommes de Sichem; et les hommes de Sichem trahirent Abimélec,
24 Allah ya yi haka saboda kisan’ya’ya saba’in na Yerub-Ba’al, don a ɗauki fansar jininsu a kan Abimelek ɗan’uwansu da kuma’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka taimake shi kisan’yan’uwansa.
afin que la violence faite aux soixante-dix fils de Jerubbaal arrive, et que leur sang retombe sur Abimélec, leur frère, qui les a tués, et sur les hommes de Sichem, qui ont fortifié ses mains pour tuer ses frères.
25 Cikin hamayya da shi waɗannan’yan ƙasar Shekem suka sa mutane a kan tuddai don su yi kwanton ɓauna a kan su yi fashi ga duk wanda ya wuce a can, wannan fa ya kai kunnen Abimelek.
Les hommes de Sichem lui tendirent une embuscade sur les sommets des montagnes et ils dévalisèrent tous ceux qui passaient par là; Abimélec en fut informé.
26 To, Ga’al ɗan Ebed ya tafi tare da’yan’uwansa zuwa Shekem,’yan ƙasarta kuwa suka dogara da shi.
Gaal, fils d'Ebed, vint avec ses frères et passa à Sichem, et les hommes de Sichem se confièrent en lui.
27 Bayan sun tafi gonaki suka tattara inabi suka matse su, sai suka yi biki a haikalin allahnsu. Yayinda suke ci da sha, sai suka la’anci Abimelek.
Ils sortirent dans les champs, moissonnèrent leurs vignes, foulèrent le raisin, firent la fête, entrèrent dans la maison de leur dieu, mangèrent et burent, et maudirent Abimélec.
28 Sa’an nan Ga’al ɗan Ebed ya ce, “Wane ne Abimelek, kuma wane ne Shekem, da za mu bauta masa? Shi ba ɗan Yerub-Ba’al ba ne, kuma ba Zebul ne mataimakinsa ba? Ku bauta wa mutanen Hamor, mahaifin Shekem! Me ya sa za mu bauta wa Abimelek?
Gaal, fils d'Ebed, dit: « Qui est Abimélec et qui est Sichem, pour que nous le servions? N'est-il pas le fils de Jerubbaal? Zebul n'est-il pas son officier? Servez les hommes de Hamor, le père de Sichem, mais pourquoi devrions-nous le servir?
29 Da a ce waɗannan mutane suna a ƙarƙashina mana! Da zan hamɓarar da shi. In ce wa Abimelek, ‘Ka tara dukan mayaƙanka!’”
Je voudrais que ce peuple soit sous ma main! Alors je supprimerais Abimélek. » Il dit à Abimélec: « Augmente ton armée et sors! »
30 Sa’ad da Zebul gwamnar birnin ya ji abin da Ga’al ɗan Ebed ya ce, sai ya fusata.
Lorsque Zebul, chef de la ville, entendit les paroles de Gaal, fils d'Ebed, sa colère s'enflamma.
31 Asirce sai ya aiki manzanni wajen Abimelek, yana cewa, “Ga’al ɗan Ebed da’yan’uwansa sun zo Shekem suna kuma zuga birnin sun tayar maka.
Il envoya des messagers à Abimélec avec ruse, en disant: « Voici que Gaal, fils d'Ebed, et ses frères sont venus à Sichem, et voici qu'ils excitent la ville contre toi.
32 To, in dare ya yi, sai ka zo da mutanenka ku yi kwanto a filaye.
Maintenant, monte de nuit, toi et le peuple qui est avec toi, et va te mettre à l'affût dans les champs.
33 Kashegari da safe, sai ku tashi ku fāɗa wa birnin. Sa’ad da Ga’al da mutanensa suka faɗa maka, sai ka yi abin da ka iya yi da su.”
Le matin, dès que le soleil sera levé, tu te lèveras de bonne heure et tu te précipiteras sur la ville. Voici, quand lui et le peuple qui est avec lui sortiront contre toi, alors tu pourras leur faire ce que tu trouveras à faire. »
34 Saboda haka Abimelek da dukan mutanensa suka tashi da dare suka ɓuya kusa da Shekem a ƙungiyoyi huɗu.
Abimélec se leva de nuit, avec tout le peuple qui était avec lui, et ils se mirent en embuscade contre Sichem en quatre compagnies.
35 To, Ga’al ɗan Ebed ya riga ya fita waje yana tsaye a ƙofar birni daidai Abimelek da mayaƙansa suka fito daga inda suka ɓuya.
Gaal, fils d'Ebed, sortit et se tint à l'entrée de la porte de la ville. Abimélec se leva de l'embuscade, avec le peuple qui était avec lui.
36 Sa’ad da Ga’al ya gan su, sai ya ce wa Zebul, “Duba, ga mutane suna gangarowa daga kan duwatsu!” Zebul ya ce, “Kana ɗaukan inuwan duwatsu kana ce mutane.”
Lorsque Gaal vit le peuple, il dit à Zebul: « Voici que des gens descendent des sommets des montagnes. » Zebul lui dit: « Tu vois les ombres des montagnes comme si elles étaient des hommes. »
37 Amma Ga’al ya sāke magana ya ce, “Duba, mutane suna gangarowa daga tsakiyar filaye, kuma wata ƙungiya tana zuwa daga wajen itacen masu duba.”
Gaal parla encore et dit: « Voici que des gens descendent par le milieu du pays, et une troupe vient par le chemin du chêne de Meonenim. »
38 Sa’an nan Zebul ya ce masa, “Ina bakin da ka yi ɗin, kai da ka ce, ‘Wane ne Abimelek da za mu bauta masa.’ Ba mutanen ne ka yi musu ba’a ba? Fita, ka yaƙe su mana!”
Alors Zebul lui dit: « Où est ta bouche, maintenant, pour que tu dises: « Qui est Abimélec, pour que nous le servions? ». N'est-ce pas là le peuple que tu as méprisé? Sors maintenant et va te battre avec eux. »
39 Saboda haka Ga’al ya fito da’yan ƙasar Shekem suka yaƙi Abimelek.
Gaal sortit devant les gens de Sichem, et il combattit Abimélec.
40 Abimelek ya kore shi, mutane da yawa suka ji ciwo a yaƙin, har zuwa ƙofar birnin.
Abimélec le poursuivit; il s'enfuit devant lui, et beaucoup de gens furent blessés, jusqu'à l'entrée de la porte.
41 Abimelek ya zauna a Aruma, Zebul kuwa ya kori Ga’al da’yan’uwansa daga Shekem.
Abimélec habitait à Aruma, et Zébul chassa Gaal et ses frères, pour qu'ils n'habitent pas à Sichem.
42 Kashegari mutanen Shekem suka tafi gonaki, aka kuwa gaya wa Abimelek.
Le lendemain, le peuple sortit dans les champs, et on en informa Abimélec.
43 Saboda haka ya ɗauki mutanensa, ya raba su ƙungiya uku, sa’an nan ya yi kwanto a gonakin. Sa’ad da ya ga mutanen suna fitowa daga birni, sai ya yi wuf ya fāɗa musu.
Celui-ci prit le peuple et le divisa en trois groupes, puis il attendit dans les champs. Il regarda, et voici que le peuple sortait de la ville. Il se leva contre eux et les frappa.
44 Abimelek da ƙungiyoyin da suke tare da shi suka yi maza suka yi tsaya a ƙofar birnin. Sa’an nan ƙungiyoyi biyu suka ruga suka fāɗa wa waɗanda suke a gonaki suka karkashe su.
Abimélec et les compagnies qui étaient avec lui se précipitèrent en avant et se tinrent à l'entrée de la porte de la ville; les deux compagnies se précipitèrent sur tous ceux qui étaient dans les champs et les frappèrent.
45 Dukan yinin, Abimelek ya matsa yaƙi da birnin sai da ya cinye ta ya kuma kashe mutanenta. Sa’an nan ya hallaka birnin ya barbaza gishiri a kanta.
Abimélec combattit la ville tout ce jour-là; il prit la ville et tua le peuple qui s'y trouvait. Il battit la ville et la sema de sel.
46 Da jin haka, sai’yan ƙasa a hasumiyar Shekem suka shiga wurin mafaka a hankalin El-Berit.
Lorsque tous les hommes de la tour de Sichem l'apprirent, ils entrèrent dans la forteresse de la maison d'Elberith.
47 Da Abimelek ya ji dukan mutanen hasumiyar Shekem sun taru a can,
On informa Abimélec que tous les hommes de la tour de Sichem étaient rassemblés.
48 sai Abimelek da dukan mutanensa suka haura zuwa Dutsen Zalmon. Sai ya ɗauki gatari ya sassare waɗansu rassa, waɗanda ya sa a kafaɗunsa. Ya umarci mutanen da suke tare da shi ya ce, “Sauri, ku yi abin da kuka ga na yi!”
Abimélec monta sur la montagne de Zalmon, lui et tout le peuple qui était avec lui. Abimélec prit une hache dans sa main, abattit un rameau des arbres, l'emporta et le posa sur son épaule. Puis il dit au peuple qui était avec lui: « Ce que vous m'avez vu faire, hâtez-vous de le faire, et faites comme moi! ».
49 Saboda haka mutanen suka sassare rassan itatuwa suka bi Abimelek. Suka tattara su a jikin mafakar suka kuma cinna mata wuta a kan mutanen da suke a ciki. Ta haka dukan mutanen da suke cikin hasumiyar Shekem, wajen maza da mata dubu ɗaya suka mutu.
Tout le peuple de même, chacun coupa sa branche, suivit Abimélec, les plaça au pied de la forteresse et mit le feu à la forteresse par-dessus, de sorte que tous les gens de la tour de Sichem moururent aussi, environ mille hommes et femmes.
50 Biye da wannan Abimelek ya tafi Tebez, ya kewaye ta ya kuma cinye ta da yaƙi.
Alors Abimélec alla à Thèbes et campa contre Thèbes, et il la prit.
51 A cikin birnin, akwai wata hasumiya mai ƙarfi, inda dukan maza da mata, dukan mutanen birnin, suka ɓuya. Suka kulle kansu, suka kuma hau rufin hasumiyar.
Mais il y avait une tour forte dans la ville, et tous les hommes et les femmes de la ville s'y réfugièrent, s'y enfermèrent et montèrent sur le toit de la tour.
52 Abimelek ya je wajen hasumiya ya kuma auka mata. Amma da ya yi kusa da ƙofar hasumiyar don yă cinna mata wuta,
Abimélec vint à la tour et la combattit; il s'approcha de la porte de la tour pour la brûler par le feu.
53 sai wata mata ta saki ɗan dutsen niƙa a kan Abimelek ta fasa ƙoƙon kansa.
Une femme jeta une meule supérieure sur la tête d'Abimélec, et lui brisa le crâne.
54 Da sauri ya kira mai riƙon masa makami ya ce, “Zaro takobinka ka kashe ni, don kada a ce ‘Mace ce ta kashe shi.’” Saboda haka bawansa ya soke shi, ya mutu.
Alors il appela en hâte le jeune homme qui portait son armure et lui dit: « Tire ton épée et tue-moi, afin qu'on ne dise pas de moi: « Une femme l'a tué ». Le jeune homme le transperça, et il mourut. »
55 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga Abimelek ya mutu, sai suka tafi gida.
Lorsque les hommes d'Israël virent qu'Abimélec était mort, ils s'en allèrent chacun à sa place.
56 Ta haka Allah ya sāka muguntar da Abimelek da ya yi wa mahaifinsa ta wurin kisan’yan’uwansa saba’in.
C'est ainsi que Dieu rendit à Abimélec la méchanceté qu'il avait commise envers son père en tuant ses soixante-dix frères.
57 Allah kuma ya sa muguntar mutanen Shekem suka koma kansu. La’anar Yotam ɗan Yerub-Ba’al kuma ta kama su.
Dieu fit retomber sur leur tête toute la méchanceté des hommes de Sichem, et la malédiction de Jotham, fils de Jerubbaal, tomba sur eux.

< Mahukunta 9 >