< Mahukunta 9 >
1 Abimelek ɗan Yerub-Ba’al ya tafi Shekem wurin’yan’uwan mahaifiyarsa, ya ce musu da kuma dukan dangin mahaifiyarsa,
Jerubba'als Søn Abimelek begav sig til sine Morbrødre i Sikem og talte til dem og til hele sin Moders Fædrenehus's Slægt og sagde:
2 “Ku tambayi’yan ƙasar Shekem, ‘Wanne ya fi muku, a sa dukan’ya’yan Yerub-Ba’al saba’in maza su yi mulkinku, ko dai mutum guda kawai yă yi mulkinku?’ Ku tuna, ni jininku ne.”
»Sig til alle Sikems Borgere: Hvad baader eder vel bedst, at halvfjerdsindstyve Mænd, alle Jerubba'als Sønner, eller at en enkelt Mand hersker over eder? Kom i Hu, at jeg er eders Kød og Blod!«
3 Sa’ad da’yan’uwan suka mayar wa’yan ƙasar Shekem wannan, sai suka goyi bayan Abimelek, gama sun ce, “Shi ɗan’uwanmu ne.”
Hans Morbrødre talte da alle disse Ord til alle Sikems Borgere til Gunst til ham; og deres Hu vendte sig til Abimelek, idet de sagde: »Han er vor Broder.«
4 Suka ba shi shekel saba’in na azurfa daga haikalin Ba’al-Berit, Abimelek kuwa ya yi amfani da shi ya yi hayar’yan tauri waɗanda suka zama masu binsa.
De gav ham derpaa halvfjerdsindstyve Sekel Sølv fra Ba'al-Berits Hus, og for dem lejede Abimelek nogle daarlige og frække Folk, som sluttede sig til ham.
5 Sai ya tafi gidan mahaifinsa a Ofra kuma a dutse guda ya kashe’yan’uwansa,’ya’yan Yerub-Ba’al. Amma Yotam, autan ɗan Yerub-Ba’al ya tsira ta wurin ɓuya.
Derpaa drog han til sin Faders Hus i Ofra og slog sine Brødre, Jerubba'als halvfjerdsindstyve Sønner, ihjel paa een Sten. Kun Jotam, Jerubba'als yngste Søn, blev tilbage, thi han havde skjult sig.
6 Sa’an nan duka’yan ƙasar Shekem da Bet Millo suka taru kusa da babban itacen wajen ginshiƙi a Shekem don a naɗa Abimelek sarki.
Derefter samledes alle Sikems Borgere og hele Millos Hus og gik hen og gjorde Abimelek til Konge ved Egen med Stenstøtten i Sikem.
7 Sa’ad da aka gaya wa Yotam wannan, sai ya hau Dutsen Gerizim ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku saurare ni,’yan ƙasar Shekem, don Allah yă saurare ku.
Da Jotam fik Efterretning herom, gik han hen og stillede sig paa Toppen af Garizims Bjerg og raabte med høj Røst til dem: »Hør mig, Sikems Borgere, saa skal Gud høre eder!
8 Wata rana itatuwa suka fita don su naɗa wa kansu sarki. Suka ce wa itacen zaitun, ‘Ka zama sarkinmu.’
Engang tog Træerne sig for at salve sig en Konge. De sagde da til Olietræet: Vær du vor Konge!
9 “Amma itacen zaitun ya ce, ‘In bar mai nawa, wanda da shi ake girmama alloli da mutane, don in zo in yi ta fama da itatuwa?’
Men Olietræet svarede dem: Skulde jeg give Afkald paa min Fedme, for hvilken Guder og Mennesker priser mig, for at give mig til at svæve over Træerne?
10 “Biye da wannan, sai itatuwan suka ce wa itacen ɓaure, ‘Zo ka zama sarkinmu.’
Saa sagde Træerne til Figentræet: Kom du og vær vor Konge!
11 “Amma itacen ɓauren ya ce, ‘In bar kyawawan’ya’yana da zaƙinsu, in zo in yi ta fama da itatuwa?’
Men Figentræet svarede dem: Skulde jeg give Afkald paa min Sødme og min liflige Frugt for at give mig til at svæve over Træerne?
12 “Sa’an nan itatuwan suka ce wa kuringar inabi, ‘Ki zo ki zama sarkinmu.’
Saa sagde Træerne til Vinstokken: Kom du og vær vor Konge!
13 “Amma kuringar ta ce, ‘In bar ruwan inabina, wanda yake faranta zuciyar alloli da mutane, in zo in yi fama da itatuwa?’
Men Vinstokken svarede dem: Skulde jeg give Afkald paa min Most, som glæder Guder og Mennesker, for at give mig til at svæve over Træerne?
14 “A ƙarshe sai dukan itatuwa suka ce wa itacen ƙaya, ‘Ka zo ka zama sarkinmu.’
Da sagde alle Træerne til Tornebusken: Kom du og vær vor Konge!
15 “Itacen ƙaya ya ce wa itatuwan, ‘In da gaske ne kuke so ku naɗa ni sarkinku, ku zo ku sha inuwana; in ba haka ba, bari wuta ta fito daga itacen ƙaya ta cinye itacen al’ul na Lebanon!’
Og Tornebusken svarede Træerne: Hvis I mener det ærligt med at salve mig til eders Konge, kom saa og søg ind under min Skygge; men hvis ikke, saa vil Flammer slaa op af Tornebusken og fortære Libanons Cedre!
16 “To, da a ce kun yi abin bangirma da aniya mai kyau sa’ad da kuka naɗa Abimelek sarki, da kun nuna wa Yerub-Ba’al da iyalinsa ladabi, da kuma kun yi masa abin da ya cancanci shi,
Hvis I nu er gaaet ærligt og redeligt til Værks, da I gjorde Abimelek til Konge, og hvis I har handlet vel mod Jerubba'al og hans Hus og gengældt ham, hvad han gjorde —
17 a yi tunani cewa mahaifina ya yi yaƙi saboda ku, ya yi kasai da ransa don yă cece ku daga hannun Midiyawa
min Fader kæmpede jo for eder og vovede sit Liv for at frelse eder af Midjaniternes Haand,
18 (amma ga shi yau kun tayar wa iyalin mahaifina, kuka kashe’ya’yansa saba’in a dutse guda, kuka kuma naɗa Abimelek, ɗan baiwa, sarki a kan’yan ƙasar Shekem domin shi ɗan’uwanku ne)
men I har i Dag rejst eder mod min Faders Hus, dræbt hans Sønner, halvfjerdsindstyve Mænd, paa een Sten og sat hans Trælkvindes Søn Abimelek til Konge over Sikems Borgere, fordi han er eders Broder —
19 in har kun aikata wannan cikin bangirma da kuma aminci wajen Yerub-Ba’al da iyalinsa a yau, bari Abimelek yă zama farin cikinku, ku kuma nasa!
ja, hvis I i Dag er gaaet ærligt og redeligt til Værks mod Jerubba'al og hans Hus, saa gid I maa faa Glæde af Abimelek, og gid han maa faa Glæde af eder;
20 Amma in ba haka ba, bari wuta ta fito daga Abimelek ya cinye ku,’yan ƙasar Shekem da Bet Millo, bari wuta kuma daga wurinku’yan ƙasar Shekem da Bet Millo ta cinye Abimelek!”
men hvis ikke, saa slaa Flammer op fra Abimelek og fortære Sikems Borgere og Millos Hus, og Flammer slaa op fra Sikems Borgere og Millos Hus og fortære Abimelek!«
21 Sa’an nan Yotam ya gudu, ya tsere zuwa Beyer ya zauna a can gama yana tsoron ɗan’uwansa Abimelek.
Derpaa tog Jotam Flugten og flygtede til Be'er; og der tog han Ophold for at være i Sikkerhed for sin Broder Abimelek.
22 Bayan Abimelek ya yi shekara uku yana mulki a Isra’ila,
Da Abimelek havde haft Magten over Israel i tre Aar,
23 sai Allah ya aiko da mugun ruhu tsakanin Abimelek da’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka ci amanar Abimelek.
sendte Gud en ond Aand mellem Abimelek og Sikems Borgere, og Sikems Borgere faldt fra Abimelek,
24 Allah ya yi haka saboda kisan’ya’ya saba’in na Yerub-Ba’al, don a ɗauki fansar jininsu a kan Abimelek ɗan’uwansu da kuma’yan ƙasar Shekem, waɗanda suka taimake shi kisan’yan’uwansa.
for at Voldsgerningen mod Jerubba'als halvfjerdsindstyve Sønner kunde blive hævnet og deres Blod komme over deres Broder Abimelek, som havde dræbt dem, og over Sikems Borgere, som havde sat ham i Stand til at dræbe sine Brødre.
25 Cikin hamayya da shi waɗannan’yan ƙasar Shekem suka sa mutane a kan tuddai don su yi kwanton ɓauna a kan su yi fashi ga duk wanda ya wuce a can, wannan fa ya kai kunnen Abimelek.
Sikems Borgere lagde da Baghold paa Bjergtoppene, og de udplyndrede alle vejfarende, der kom forbi dem. Dette meldtes Abimelek.
26 To, Ga’al ɗan Ebed ya tafi tare da’yan’uwansa zuwa Shekem,’yan ƙasarta kuwa suka dogara da shi.
Nu kom Ga'al, Ebeds Søn, med sine Brødre og flyttede ind i Sikem; og Sikems Borgere fattede Tillid til ham.
27 Bayan sun tafi gonaki suka tattara inabi suka matse su, sai suka yi biki a haikalin allahnsu. Yayinda suke ci da sha, sai suka la’anci Abimelek.
De begav sig ud i Marken, plukkede Druer og pressede dem og fejrede deres Vinhøstfest. Og de gik ind i deres Guds Hus, hvor de spiste og drak og udstødte Forbandelser over Abimelek.
28 Sa’an nan Ga’al ɗan Ebed ya ce, “Wane ne Abimelek, kuma wane ne Shekem, da za mu bauta masa? Shi ba ɗan Yerub-Ba’al ba ne, kuma ba Zebul ne mataimakinsa ba? Ku bauta wa mutanen Hamor, mahaifin Shekem! Me ya sa za mu bauta wa Abimelek?
Da sagde Ga'al, Ebeds Søn: »Hvem er Abimelek, og hvad er Sikem, at vi skal være hans Trælle! Var ikke Jerubba'als Søn og hans Foged Zebul Trælle for Hamors, Sikems Faders, Mænd hvorfor skal vi da være hans Trælle?
29 Da a ce waɗannan mutane suna a ƙarƙashina mana! Da zan hamɓarar da shi. In ce wa Abimelek, ‘Ka tara dukan mayaƙanka!’”
Havde jeg blot Magten over Folket her, skulde jeg nok skaffe Abimelek af Vejen!«
30 Sa’ad da Zebul gwamnar birnin ya ji abin da Ga’al ɗan Ebed ya ce, sai ya fusata.
Da Zebul, Byens Høvedsmand, hørte Ga'als, Ebeds Søns, Ord, blussede hans Vrede op,
31 Asirce sai ya aiki manzanni wajen Abimelek, yana cewa, “Ga’al ɗan Ebed da’yan’uwansa sun zo Shekem suna kuma zuga birnin sun tayar maka.
og han sendte Bud til Abimelek i Aruma og lod sige: »Se, Ga'al, Ebeds Søn, og hans Brødre er kommet til Sikem, og se, de ophidser Byen imod dig; forstærk derfor din Hær og ryk ud!
32 To, in dare ya yi, sai ka zo da mutanenka ku yi kwanto a filaye.
Og nu, bryd op ved Nattetide med dine Folk og læg dig i Baghold paa Marken;
33 Kashegari da safe, sai ku tashi ku fāɗa wa birnin. Sa’ad da Ga’al da mutanensa suka faɗa maka, sai ka yi abin da ka iya yi da su.”
og kast dig saa over Byen tidligt om Morgenen, naar Solen staar op! Naar da han og hans Folk rykker ud imod dig, kan du gøre med dem, hvad der falder for!«
34 Saboda haka Abimelek da dukan mutanensa suka tashi da dare suka ɓuya kusa da Shekem a ƙungiyoyi huɗu.
Abimelek brød da op ved Nattetide med alle sine Folk, og de lagde sig i Baghold imod Sikem i fire Afdelinger.
35 To, Ga’al ɗan Ebed ya riga ya fita waje yana tsaye a ƙofar birni daidai Abimelek da mayaƙansa suka fito daga inda suka ɓuya.
Da gik Ga'al, Ebeds Søn, ned og stillede sig op ved Byporten. Og Abimelek og hans Folk rejste sig fra deres Baghold.
36 Sa’ad da Ga’al ya gan su, sai ya ce wa Zebul, “Duba, ga mutane suna gangarowa daga kan duwatsu!” Zebul ya ce, “Kana ɗaukan inuwan duwatsu kana ce mutane.”
Da Ga'al fik Øje paa Folkene, sagde han til Zebul: »Se, der stiger Folk ned fra Bjergtoppene!« Men Zebul sagde til ham: »Det er Bjergenes Skygge, du tager for Mænd!«
37 Amma Ga’al ya sāke magana ya ce, “Duba, mutane suna gangarowa daga tsakiyar filaye, kuma wata ƙungiya tana zuwa daga wajen itacen masu duba.”
Men Ga'al sagde atter: »Der stiger Folk ned fra Landets Navle, og en anden Skare kommer i Retning af Sandsigernes Træ!«
38 Sa’an nan Zebul ya ce masa, “Ina bakin da ka yi ɗin, kai da ka ce, ‘Wane ne Abimelek da za mu bauta masa.’ Ba mutanen ne ka yi musu ba’a ba? Fita, ka yaƙe su mana!”
Da sagde Zebul til ham: »Hvor er nu dine store Ord fra før: Hvem er Abimelek, at vi skal være hans Trælle? Der er de Folk, du lod haant om — ryk nu ud og kæmp med dem!«
39 Saboda haka Ga’al ya fito da’yan ƙasar Shekem suka yaƙi Abimelek.
Ga'al rykkede da ud i Spidsen for Sikems Borgere for at kæmpe mod Abimelek.
40 Abimelek ya kore shi, mutane da yawa suka ji ciwo a yaƙin, har zuwa ƙofar birnin.
Men Abimelek slog ham paa Flugt, og mange faldt og laa dræbte helt hen til Byporten.
41 Abimelek ya zauna a Aruma, Zebul kuwa ya kori Ga’al da’yan’uwansa daga Shekem.
Abimelek tog saa Ophold i Aruma; og Zebul jog Ga'al og hans Brødre bort fra Sikem.
42 Kashegari mutanen Shekem suka tafi gonaki, aka kuwa gaya wa Abimelek.
Næste Dag begav Folket sig ud paa Marken, og det meldtes Abimelek.
43 Saboda haka ya ɗauki mutanensa, ya raba su ƙungiya uku, sa’an nan ya yi kwanto a gonakin. Sa’ad da ya ga mutanen suna fitowa daga birni, sai ya yi wuf ya fāɗa musu.
Han tog da sine Folk og delte dem i tre dele og lagde Baghold paa Marken; og da han saa Folket drage ud, overfaldt han dem og slog dem.
44 Abimelek da ƙungiyoyin da suke tare da shi suka yi maza suka yi tsaya a ƙofar birnin. Sa’an nan ƙungiyoyi biyu suka ruga suka fāɗa wa waɗanda suke a gonaki suka karkashe su.
Og Abimelek og den Afdeling, han havde hos sig, brød frem og tog Stilling ved Indgangen til Byen, medens de to andre Afdelinger kastede sig over alle dem, der var ude paa Marken; og huggede dem ned;
45 Dukan yinin, Abimelek ya matsa yaƙi da birnin sai da ya cinye ta ya kuma kashe mutanenta. Sa’an nan ya hallaka birnin ya barbaza gishiri a kanta.
og efter at Abimelek hele Dagen igennem havde angrebet Byen, indtog han den, dræbte Folkene deri, nedbrød Byen og strøede Salt paa den.
46 Da jin haka, sai’yan ƙasa a hasumiyar Shekem suka shiga wurin mafaka a hankalin El-Berit.
Da hele Besætningen i Sikems Taarn hørte det, begav de sig ben til Kælderrummet i El-Berits Hus.
47 Da Abimelek ya ji dukan mutanen hasumiyar Shekem sun taru a can,
Og da Abimelek fik Melding om, at hele Besætningen i Sikems Taarn var samlet,
48 sai Abimelek da dukan mutanensa suka haura zuwa Dutsen Zalmon. Sai ya ɗauki gatari ya sassare waɗansu rassa, waɗanda ya sa a kafaɗunsa. Ya umarci mutanen da suke tare da shi ya ce, “Sauri, ku yi abin da kuka ga na yi!”
gik han med alle sine Folk op paa Zalmonbjerget. Her greb han en Økse, afhuggede et Knippe Grene, løftede det op og tog det paa Skulderen; og han sagde til sine Folk: »Skynd eder at gøre det samme, som I saa, jeg gjorde!«
49 Saboda haka mutanen suka sassare rassan itatuwa suka bi Abimelek. Suka tattara su a jikin mafakar suka kuma cinna mata wuta a kan mutanen da suke a ciki. Ta haka dukan mutanen da suke cikin hasumiyar Shekem, wajen maza da mata dubu ɗaya suka mutu.
Alle Folkene afhuggede da ogsaa hver sit Knippe og fulgte efter Abimelek og lagde det oven paa Kælderrummet og stak Ild paa Kælderrummet oven over dem. Saaledes omkom ogsaa hele Besætningen i Sikems Taarn, henved 1000 Mænd og Kvinder.
50 Biye da wannan Abimelek ya tafi Tebez, ya kewaye ta ya kuma cinye ta da yaƙi.
Derefter drog Abimelek mod Tebez, og han belejrede Byen og indtog den.
51 A cikin birnin, akwai wata hasumiya mai ƙarfi, inda dukan maza da mata, dukan mutanen birnin, suka ɓuya. Suka kulle kansu, suka kuma hau rufin hasumiyar.
Inde i Byen var der et stærkt befæstet Taarn; derhen flygtede alle Mænd og Kvinder, alle Byens Indbyggere, idet de stængede efter sig og tyede op paa Taarnets Tag;
52 Abimelek ya je wajen hasumiya ya kuma auka mata. Amma da ya yi kusa da ƙofar hasumiyar don yă cinna mata wuta,
Abimelek rykkede da frem til Taarnet og angreb det; men da han nærmede sig Taarnets Indgang for at stikke Ild derpaa,
53 sai wata mata ta saki ɗan dutsen niƙa a kan Abimelek ta fasa ƙoƙon kansa.
kastede en Kvinde en Møllesten ned paa Abimeleks Hoved og knuste hans Hjerneskal.
54 Da sauri ya kira mai riƙon masa makami ya ce, “Zaro takobinka ka kashe ni, don kada a ce ‘Mace ce ta kashe shi.’” Saboda haka bawansa ya soke shi, ya mutu.
Da raabte han i Hast til sin Vaabendrager: »Drag dit Sværd og dræb mig, for at det ikke skal siges, at en Kvinde har slaaet mig ihjel!« Og Vaabendrageren gennemborede ham, saa han døde.
55 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga Abimelek ya mutu, sai suka tafi gida.
Men da Israeliterne saa, at Abimelek var død, begav de sig hver til sit.
56 Ta haka Allah ya sāka muguntar da Abimelek da ya yi wa mahaifinsa ta wurin kisan’yan’uwansa saba’in.
Saaledes gengældte Gud det onde, Abimelek havde øvet mod sin Fader ved at dræbe sine halvfjerdsindstyve Brødre;
57 Allah kuma ya sa muguntar mutanen Shekem suka koma kansu. La’anar Yotam ɗan Yerub-Ba’al kuma ta kama su.
og al Sikemiternes Ondskab lod Gud komme over deres egne Hoveder. Paa den Maade kom Jotams, Jerubba'als Søns, Forbandelse over dem.