< Mahukunta 8 >

1 To, mutanen Efraim suka ce wa Gideyon, “Me ya sa ka yi mana haka? Me ya sa ba ka kira mu lokacin da ka tafi yaƙi da Midiyawa ba?” Suka zarge shi sosai.
Then the descendants of Ephraim said to Gideon, “Why have you acted toward us like this? When you went out to fight against the people of Midian, why did you not summon us [to help you]?” They rebuked Gideon severely.
2 Amma ya ce musu, “Me na yi da za a iya kwatanta da abin da kuka yi? Ashe, kalar inabin da Efraim ta yi bai fi dukan girbin inabin da Abiyezer suka yi ba?
But Gideon replied, “I have done [RHQ] very little compared with what you have done! My small clan of descendants of Abiezer only started the battle, but [your very large group of] descendants of Ephraim [helped me to finish the task very well. It is like] the final grapes of the harvest being much better than the first grapes that are picked.
3 Allah ya ba da Oreb da Zeyib, shugabannin Midiyawa a hannuwanku. Me na yi da ya fi naku? Da ya faɗi haka sai hankalinsu ya kwanta.”
God enabled you to defeat Oreb and Zeeb, the generals of the army from Midian. That is [RHQ] much more important than what I did!” After Gideon told them that, they no longer resented what he had done.
4 Gideyon da mutanensa ɗari uku, sun gaji, duk da haka suka yi ta fafarar, suka zo Urdun suka haye shi.
Then Gideon and his 300 men [went east and] crossed the Jordan [River]. Although they were very tired, they continued to pursue their enemies.
5 Ya ce wa mutanen Sukkot, “Ku ba wa mutanena burodi; sun gaji, har yanzu ina fafarar Zeba da Zalmunna, sarakunan Midiyawa.”
When they arrived at Succoth [town], Gideon said to the town leaders, “Please give my men some food! They are very tired. We are pursuing Zebah and Zalmunna, the kings of Midian.”
6 Amma shugabannin Sukkot suka ce, “Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Don me za mu ba wa mayaƙanka burodi?”
But the leaders of Succoth replied, “You have not caught [RHQ] Zebah and Zalmunna yet. So why should we give food to your troops [now? Catch them first, and then we will give you food].”
7 Sai Gideyon ya ce, “Haka ko? To, sa’ad da Ubangiji ya ba da Zeba da Zalmunna a hannuna, zan tsattsaga jikinku da ƙayayyuwan jeji.”
Gideon replied, “[Because you said that], after Yahweh enables us to defeat Zebah and Zalmunna, we will return. And then we will make whips from thorns from the desert, and with them we will rip the flesh off your bones!”
8 Daga nan ya wuce zuwa Fenuwel ya yi irin roƙon nan, amma suka amsa yadda mutanen Sukkot suka yi.
From there, Gideon [and his 300 men] went to Peniel and asked for food there, but the people gave him the same answer.
9 Saboda haka sai ya ce wa mutanen Fenuwel, “Sa’ad da na dawo da nasara zan rushe wannan hasumiya.”
So he said to the men of Peniel, “After I defeat those kings, I will return and tear down this tower!”
10 To, Zeba da Zalmunna suna a Karkor da mayaƙa wajen dubu goma sha biyar, abin da ya rage ke nan na mayaƙan gabashi; mayaƙa masu takobi dubu ɗari da ashirin ne suka mutu.
By that time, Zebah and Zalmunna had gone to Karkor [town] with 15,000 troops. They were all that were left of the armies that had come from the east. 120,000 of their men had already been killed.
11 Gideyon ya haura ta hanyar makiyaya, gabas da Noba, da kuma Yogbeha, ya fāɗa wa mayaƙan ta yadda ba su zata ba.
Gideon [and his men] went east along the road on which caravans travel. They went past Nobah and Jogbehah [villages] and arrived at the enemy camp by surprise.
12 Zeba da Zalmunna, sarakunan biyu na Midiyawa suka tsere, amma ya bi su ya kama, ya fatattaki dukan mayaƙansu.
Zebah and Zalmunna fled, but Gideon’s men pursued them and captured them and all their warriors.
13 Sa’an nan Gideyon ɗan Yowash ya komo daga yaƙi ta Hanyar Heres.
After that, Gideon and his men [took Zebah and Zalmunna with them and] started to return, going through Heres Pass.
14 Ya kama wani saurayin Sukkot ya tambaye shi, saurayin kuwa ya rubuta masa dukan sunayen shugabanni saba’in da bakwai na Sukkot, da dattawan garin.
There he captured a young man from Succoth, and demanded that he write down the names of all of the leaders in the town. The young man wrote down seventy-seven names.
15 Sa’an nan Gideyon ya zo ya ce wa mutanen Sukkot, “To, ga Zeba da Zalmunna, waɗanda kuka yi mini ba’a kuna cewa, ‘Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Me zai sa mu ba mutanenka da suka gaji burodi?’”
Then Gideon and his men returned to Succoth and said to those leaders, “Here are Zebah and Zalmunna. When we were here before, you made fun of me and said ‘You have not [RHQ] caught Zebah and Zalmunna yet! After you catch them, we will give your exhausted men some food.’”
16 Ya kwashe dattawan garin ya koya wa mutanen Sukkot hankali ta wurin hukunta su da ƙayayyuwan hamada.
Then Gideon’s men took the town leaders and whipped them with whips made from briers from the desert, to teach them [that they deserved to be punished for not giving them any food].
17 Ya rushe hasumiyar Fenuwel ya kuma karkashe mutanen garin.
Then [they went to] Peniel and tore down the tower, and killed all the men in the town.
18 Sa’an nan ya ce wa Zeba da Zalmunna, “Waɗanne irin mutane ne kuka karkashe a Tabor.” Suka ce, “Mutane kamar ka ne kowane kamar ɗan sarki.”
Then Gideon said to Zebah and Zalmunna, “The men you killed near Tabor [Mountain], what did they look like?” They replied, “They were like you; they all looked like they were sons of a king.”
19 Gideyon ya ce, “Waɗannan’yan’uwana ne,’ya’yan mahaifiyata. Muddin Ubangiji yana a raye, da a ce kun bar su da rai, da ba zan kashe ku ba.”
Gideon replied, “They were my brothers! Just as surely as Yahweh lives, I would not kill you if you had not killed them.”
20 Da ya juya wajen Yeter, ɗan farinsa, sai ya ce, “Ka kashe su!” Amma Yeter bai zāre takobinsa ba, domin shi yaro ne kawai kuma yana tsoro.
Then he turned to his oldest son, Jether. He said to him, “Kill them!” But Jether was only a boy, and he was afraid, so he did not pull out his dagger [to kill them].
21 Zeba da Zalmunna suka ce masa, “Zo, ka yi da kanka. ‘Yadda mutum yake haka ƙarfinsa.’” Ta haka Gideyon ya matso gaba ya kashe su, ya ɗauki kayan ado daga wuyar raƙumansu.
Then Zebah and Zalmunna said to Gideon, “Do not ask a young boy to do the work that a man should do!” So Gideon killed both of them. Then he took the gold ornaments from the necks of their camels.
22 Isra’ilawa suka ce wa Gideyon, “Ka yi mulkinmu, kai, ɗanka da jikanka, domin ka cece mu daga hannun Midiyawa.”
Then a group of Israeli men [came to] Gideon and said to him, “You be our ruler! [We want] you and your son and your grandsons [to] be our rulers, because you rescued us from the Midian army.”
23 Amma Gideyon ya ce musu, “Ni, ko ɗana, ba za mu yi mulkinku ba. Ubangiji ne zai yi mulkinku.”
But Gideon replied, “No, I will not rule over you, and my son will not rule over you. Yahweh will rule over you.”
24 Kuma ya ce, “Ina da roƙo guda ɗaya, cewa kowannenku ya ba ni’yan kunne daga rabon ganima.” (Al’adar mutanen Ishmayel ce su sa’yan kunnen zinariya.)
Then he said, “I request only one thing. I request that each of you give me one earring from the things you captured after the battle.” [All the men descended from Ishmael wore gold earrings.]
25 Suka ce, “Za mu yi farin cikin ba ka su.” Saboda haka suka shimfiɗa mayafi, kowanne ya sa ɗan kunne ɗaya daga ganimar.
They replied, “We will be glad to give earrings to you!” So they spread a cloth [on the ground], and each man threw on it one gold earring that he had taken [from a man he had killed in the battle].
26 Nauyin’yan kunnen zinariyar ya kai shekel ɗari goma sha bakwai, ban da kayan ado, abin wuya da tufafin shunayya waɗanda sarakuna Midiyawa suke sawa ko sarƙoƙin da suke wuyar raƙumansu.
The weight of all the earrings was (43 pounds/19.4 kg.). That did not include other things [that they gave to Gideon]—the other ornaments or the pendants or the clothes that the kings of Midian wore or the gold chains that were on the necks of their camels.
27 Gideyon ya efod da zinariyar, wanda ya ajiye a Ofra, garinsa. Dukan Isra’ila suka shiga yin karuwanci ta wurin yin sujada a can, ya kuwa zama wa Gideyon da dukan iyalinsa tarko.
Gideon made/decorated a sacred vest from the gold, and later he put it in his hometown, Ophrah. But soon the Israeli people started to worship the vest. So it became like a trap [MET] for the people, [causing them to worship it instead of worshiping only God].
28 Da haka Isra’ilawa suka mallaki Midiyawa ba su kuma sāke tā da kai ba. A zamanin Gideyon ƙasar ta sami zaman lafiya har shekara arba’in.
That is how the Israelis defeated the people from Midian. The people of Midian did not become strong enough to attack Israel again. So while Gideon was alive, there was peace in the land for 40 years.
29 Yerub-Ba’al ɗan Yowash ya koma gida don yă zauna.
Gideon went back home to live there.
30 Yana da’ya’ya saba’in maza da ya haifa, gama yana da mata da yawa.
He had many wives, and they bore him seventy sons.
31 Yana kuma da ƙwarƙwara wadda take Shekem, ita ma ta haifa masa ɗa wanda ya ba shi suna Abimelek.
He also had a slave wife in Shechem [town], who bore him a son whom he named Abimelech.
32 Gideyon ɗan Yowash ya rasu da kyakkyawan tsufa aka kuma binne shi a kabarin Yowash mahaifinsa a Ofra na mutanen Abiyezer.
Gideon died when he was very old. They buried his body in the grave where his father Joash was buried, at Ophrah, in the land belonging to the descendants of Abiether.
33 Ba a daɗe da rasuwar Gideyon ba, sai Isra’ila ta sāke shiga karuwanci suna bauta wa Ba’al. Suka kafa Ba’al-Berit yă zama musu allahnsu ba kuma
But as soon as Gideon died, the Israelis [stopped worshiping God and started worshiping the images of the god Baal, like] [MET] adultresses [leave their husbands and go to sleep with other men]. They made a [statue of a] new god called Baal-Berith.
34 tuna da Ubangiji Allahnsu, wanda ya cece su daga hannuwan abokan gābansu a kowane gefe ba.
They forgot about Yahweh, the one who had rescued them from all their enemies that surrounded them.
35 Suka kāsa nuna alheri ga gidan Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) saboda abubuwa masu alherin da ya yi musu.
And even though Gideon had done many good things for the Israelis, they were not kind to Gideon’s family.

< Mahukunta 8 >