< Mahukunta 8 >

1 To, mutanen Efraim suka ce wa Gideyon, “Me ya sa ka yi mana haka? Me ya sa ba ka kira mu lokacin da ka tafi yaƙi da Midiyawa ba?” Suka zarge shi sosai.
And the men of Ephraim said unto him, What is this thing that thou hast done unto us, not to call for us, when thou wentest to fight with the Midianites? And they quarrelled with him vehemently.
2 Amma ya ce musu, “Me na yi da za a iya kwatanta da abin da kuka yi? Ashe, kalar inabin da Efraim ta yi bai fi dukan girbin inabin da Abiyezer suka yi ba?
And he said unto them, What have I done now in comparison with you? Is not the gleaning of Ephraim better than the vintage of Abi'ezer?
3 Allah ya ba da Oreb da Zeyib, shugabannin Midiyawa a hannuwanku. Me na yi da ya fi naku? Da ya faɗi haka sai hankalinsu ya kwanta.”
Into your hand God delivered the princes of Midian, 'Oreb and Zeeb: and what have I been able to do in comparison with you? Then was their anger abated from him, when he had spoken this speech.
4 Gideyon da mutanensa ɗari uku, sun gaji, duk da haka suka yi ta fafarar, suka zo Urdun suka haye shi.
And Gid'on came to the Jordan, and passed over, he, and the three hundred men that were with him, faint, and in pursuit.
5 Ya ce wa mutanen Sukkot, “Ku ba wa mutanena burodi; sun gaji, har yanzu ina fafarar Zeba da Zalmunna, sarakunan Midiyawa.”
And he said unto the men of Succoth, Give, I pray you, a few loaves of bread unto the people that are in my train; for they are faint, and I am pursuing after Zebach and Zalmunna,' the kings of Midian.
6 Amma shugabannin Sukkot suka ce, “Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Don me za mu ba wa mayaƙanka burodi?”
And the princes of Succoth said, Is the sole of the foot of Zebach and Zalmunna' now already in thy hand, that we should give unto thy army bread?
7 Sai Gideyon ya ce, “Haka ko? To, sa’ad da Ubangiji ya ba da Zeba da Zalmunna a hannuna, zan tsattsaga jikinku da ƙayayyuwan jeji.”
And Gid'on said, Therefore when the Lord hath delivered Zebach and Zalmunna' into my hand, then will I thresh your flesh with the thorns of the wilderness and with briers.
8 Daga nan ya wuce zuwa Fenuwel ya yi irin roƙon nan, amma suka amsa yadda mutanen Sukkot suka yi.
And he went up thence to Penuel, and spoke unto them in the same manner: and the men of Penuel answered him as the men of Succoth had answered.
9 Saboda haka sai ya ce wa mutanen Fenuwel, “Sa’ad da na dawo da nasara zan rushe wannan hasumiya.”
And he said also unto the men of Penuel thus, When I return again in peace, I will break down this tower.
10 To, Zeba da Zalmunna suna a Karkor da mayaƙa wajen dubu goma sha biyar, abin da ya rage ke nan na mayaƙan gabashi; mayaƙa masu takobi dubu ɗari da ashirin ne suka mutu.
Now Zebach and Zalmunna' were in Karkor, and their camps with them, about fifteen thousand men, all that had been left of all the camp of the children of the east; but those who had fallen were one hundred and twenty thousand men that drew the sword.
11 Gideyon ya haura ta hanyar makiyaya, gabas da Noba, da kuma Yogbeha, ya fāɗa wa mayaƙan ta yadda ba su zata ba.
And Gid'on went up by the way of those that dwelt in tents, to the east of Nobach and Yogbehah, and smote the camp; but the camp thought itself secure.
12 Zeba da Zalmunna, sarakunan biyu na Midiyawa suka tsere, amma ya bi su ya kama, ya fatattaki dukan mayaƙansu.
And Zebach and Zalmunna' fled; but he pursued after them, and captured the two kings of Midian, Zebach and Zalmunna', and all the camp he discomfited.
13 Sa’an nan Gideyon ɗan Yowash ya komo daga yaƙi ta Hanyar Heres.
And Gid'on the son of Joash returned from the battle before the rising of the sun,
14 Ya kama wani saurayin Sukkot ya tambaye shi, saurayin kuwa ya rubuta masa dukan sunayen shugabanni saba’in da bakwai na Sukkot, da dattawan garin.
And he caught a young man of the people of Succoth, and inquired of him: and he wrote down for him the princes of Succoth, and the elders thereof, seventy and seven men.
15 Sa’an nan Gideyon ya zo ya ce wa mutanen Sukkot, “To, ga Zeba da Zalmunna, waɗanda kuka yi mini ba’a kuna cewa, ‘Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Me zai sa mu ba mutanenka da suka gaji burodi?’”
And he came unto the men of Succoth, and said, Behold here are Zebach and Zalmunna', with whom ye derided me, saying, Is the sole of the foot of Zebach and Zalmunna' now already in thy hand, that we should give unto thy weary men bread?
16 Ya kwashe dattawan garin ya koya wa mutanen Sukkot hankali ta wurin hukunta su da ƙayayyuwan hamada.
And he took the elders of the city, and the thorns of the wilderness and briers, and chastised with them the men of Succoth.
17 Ya rushe hasumiyar Fenuwel ya kuma karkashe mutanen garin.
And the tower of Penuel he beat down, and slew the men of the city.
18 Sa’an nan ya ce wa Zeba da Zalmunna, “Waɗanne irin mutane ne kuka karkashe a Tabor.” Suka ce, “Mutane kamar ka ne kowane kamar ɗan sarki.”
And he said unto Zebach and Zalmunna', What kind of men were those whom ye slew at Tabor! And they answered, As thou art, so were they; one was in form like that of the children of a king.
19 Gideyon ya ce, “Waɗannan’yan’uwana ne,’ya’yan mahaifiyata. Muddin Ubangiji yana a raye, da a ce kun bar su da rai, da ba zan kashe ku ba.”
And he said, They were my brothers, the sons of my mother; as the Lord liveth, if ye had spared them alive, I would not slay you.
20 Da ya juya wajen Yeter, ɗan farinsa, sai ya ce, “Ka kashe su!” Amma Yeter bai zāre takobinsa ba, domin shi yaro ne kawai kuma yana tsoro.
And he said unto Yether his first-born, Rise up, and slay them. But the youth drew not his sword; for he was afraid, because he was yet a youth.
21 Zeba da Zalmunna suka ce masa, “Zo, ka yi da kanka. ‘Yadda mutum yake haka ƙarfinsa.’” Ta haka Gideyon ya matso gaba ya kashe su, ya ɗauki kayan ado daga wuyar raƙumansu.
Then said Zebach and Zalmunna', Rise thou, and fall upon us; for as the man is, so is his strength. And Gid'on arose, and slew Zebach and Zalmunna'; and he took away the crescent ornaments that were on the necks of their camels.
22 Isra’ilawa suka ce wa Gideyon, “Ka yi mulkinmu, kai, ɗanka da jikanka, domin ka cece mu daga hannun Midiyawa.”
And the men of Israel said unto Gid'on, Rule thou over us, both thou and thy son, and thy son's son also; for thou hast delivered us out of the hand of Midian.
23 Amma Gideyon ya ce musu, “Ni, ko ɗana, ba za mu yi mulkinku ba. Ubangiji ne zai yi mulkinku.”
And Gid'on said unto them, I will not rule over you, neither shall my son rule over you: the Lord shall rule over you.
24 Kuma ya ce, “Ina da roƙo guda ɗaya, cewa kowannenku ya ba ni’yan kunne daga rabon ganima.” (Al’adar mutanen Ishmayel ce su sa’yan kunnen zinariya.)
And Gid'on said unto them, I would ask one request of you, that ye should give me every man the earring of his booty; for they had had golden earrings, because they were Ishmaelites.
25 Suka ce, “Za mu yi farin cikin ba ka su.” Saboda haka suka shimfiɗa mayafi, kowanne ya sa ɗan kunne ɗaya daga ganimar.
And they answered, We will willingly give. And they spread out a garment, and they cast therein every man the earring of his booty.
26 Nauyin’yan kunnen zinariyar ya kai shekel ɗari goma sha bakwai, ban da kayan ado, abin wuya da tufafin shunayya waɗanda sarakuna Midiyawa suke sawa ko sarƙoƙin da suke wuyar raƙumansu.
And the weight of the golden earrings that he had requested was a thousand and seven hundred shekels of gold; besides the crescent ornaments, and ear-drops, and purple garments that were on the kings of Midian, and besides the chains that were about their camels' necks.
27 Gideyon ya efod da zinariyar, wanda ya ajiye a Ofra, garinsa. Dukan Isra’ila suka shiga yin karuwanci ta wurin yin sujada a can, ya kuwa zama wa Gideyon da dukan iyalinsa tarko.
And Gid'on made thereof an ephod, and set it up in his city, in 'Ophrah: and all Israel went astray after it thither; and it became a snare unto Gid'on, and to his house.
28 Da haka Isra’ilawa suka mallaki Midiyawa ba su kuma sāke tā da kai ba. A zamanin Gideyon ƙasar ta sami zaman lafiya har shekara arba’in.
And Midian was humbled before the children of Israel, so that they lifted not up their head any more. And the country was quiet forty years in the days of Gid'on.
29 Yerub-Ba’al ɗan Yowash ya koma gida don yă zauna.
And Yerubba'al the son of Joash went and dwelt in his own house.
30 Yana da’ya’ya saba’in maza da ya haifa, gama yana da mata da yawa.
And Gid'on had seventy sons begotten of his body; for he had many wives.
31 Yana kuma da ƙwarƙwara wadda take Shekem, ita ma ta haifa masa ɗa wanda ya ba shi suna Abimelek.
And his concubine that was in Shechem, she also bore him a son, and he gave him the name, Abimelech.
32 Gideyon ɗan Yowash ya rasu da kyakkyawan tsufa aka kuma binne shi a kabarin Yowash mahaifinsa a Ofra na mutanen Abiyezer.
And Gid'on the son of Joash died in a good old age, and was buried in the sepulchre of Joash his father, in 'Ophrah of the Abi'ezrites.
33 Ba a daɗe da rasuwar Gideyon ba, sai Isra’ila ta sāke shiga karuwanci suna bauta wa Ba’al. Suka kafa Ba’al-Berit yă zama musu allahnsu ba kuma
And it came to pass, when Gid'on was dead, that the children of Israel turned again, and went astray after the Be'alim, and made themselves Ba'al-berith for a god.
34 tuna da Ubangiji Allahnsu, wanda ya cece su daga hannuwan abokan gābansu a kowane gefe ba.
And the children of Israel remembered not the Lord their God, who delivered them out of the hand of all their enemies on every side.
35 Suka kāsa nuna alheri ga gidan Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) saboda abubuwa masu alherin da ya yi musu.
Neither showed they kindness to the house of Yerubba'al, namely, Gid'on, in accordance with all the good which he had done unto Israel.

< Mahukunta 8 >