< Mahukunta 8 >

1 To, mutanen Efraim suka ce wa Gideyon, “Me ya sa ka yi mana haka? Me ya sa ba ka kira mu lokacin da ka tafi yaƙi da Midiyawa ba?” Suka zarge shi sosai.
And the men of Ephraim came and said to him, Why did you not send for us when you went to war against Midian? And they said sharp and angry words to him.
2 Amma ya ce musu, “Me na yi da za a iya kwatanta da abin da kuka yi? Ashe, kalar inabin da Efraim ta yi bai fi dukan girbin inabin da Abiyezer suka yi ba?
And he said to them, What have I done in comparison with you? Is not that which Ephraim took up after the grape-cutting better than all the grapes which Abiezer got in from the grape-cutting?
3 Allah ya ba da Oreb da Zeyib, shugabannin Midiyawa a hannuwanku. Me na yi da ya fi naku? Da ya faɗi haka sai hankalinsu ya kwanta.”
God has given into your hands the chiefs of Midian, Oreb and Zeeb; what have I been able to do in comparison with you? And when he said this, their feeling about him became kinder.
4 Gideyon da mutanensa ɗari uku, sun gaji, duk da haka suka yi ta fafarar, suka zo Urdun suka haye shi.
Then Gideon came to Jordan and went over it with his three hundred, overcome with weariness and in need of food.
5 Ya ce wa mutanen Sukkot, “Ku ba wa mutanena burodi; sun gaji, har yanzu ina fafarar Zeba da Zalmunna, sarakunan Midiyawa.”
And he said to the men of Succoth, Give bread cakes to my people, for they are overcome with weariness, and I am going on after Zebah and Zalmunna, the kings of Midian.
6 Amma shugabannin Sukkot suka ce, “Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Don me za mu ba wa mayaƙanka burodi?”
But the chiefs of Succoth said, Are the hands of Zebah and Zalmunna even now in your hand that we are to give bread to your army?
7 Sai Gideyon ya ce, “Haka ko? To, sa’ad da Ubangiji ya ba da Zeba da Zalmunna a hannuna, zan tsattsaga jikinku da ƙayayyuwan jeji.”
Then Gideon said, Because of this, when the Lord has given Zebah and Zalmunna into my hands, I will have you stretched on a bed of thorns of the waste land and on sharp stems, and have you crushed as grain is crushed on a grain-floor.
8 Daga nan ya wuce zuwa Fenuwel ya yi irin roƙon nan, amma suka amsa yadda mutanen Sukkot suka yi.
So he went up from there to Penuel and made the same request to the men of Penuel; but they gave him the same answer as the men of Succoth had given.
9 Saboda haka sai ya ce wa mutanen Fenuwel, “Sa’ad da na dawo da nasara zan rushe wannan hasumiya.”
So he said to the men of Penuel, When I come back in peace, I will have this tower broken down.
10 To, Zeba da Zalmunna suna a Karkor da mayaƙa wajen dubu goma sha biyar, abin da ya rage ke nan na mayaƙan gabashi; mayaƙa masu takobi dubu ɗari da ashirin ne suka mutu.
Now Zebah and Zalmunna were in Karkor and their armies with them, about fifteen thousand men, those of all the army of the children of the east who were still living; for a hundred and twenty thousand of their swordsmen had been put to death.
11 Gideyon ya haura ta hanyar makiyaya, gabas da Noba, da kuma Yogbeha, ya fāɗa wa mayaƙan ta yadda ba su zata ba.
And Gideon went up by the way used by the people living in tents on the east of Nobah and Jogbehah, and made an attack on the army when they had no thought of danger.
12 Zeba da Zalmunna, sarakunan biyu na Midiyawa suka tsere, amma ya bi su ya kama, ya fatattaki dukan mayaƙansu.
And Zebah and Zalmunna went in flight; and he went after them, and took the two kings of Midian, Zebah and Zalmunna, and put all the army to the curse.
13 Sa’an nan Gideyon ɗan Yowash ya komo daga yaƙi ta Hanyar Heres.
Then Gideon, the son of Joash, went back from the fight:
14 Ya kama wani saurayin Sukkot ya tambaye shi, saurayin kuwa ya rubuta masa dukan sunayen shugabanni saba’in da bakwai na Sukkot, da dattawan garin.
And taking prisoner a young man of the people of Succoth, he got from him, in answer to his questions, a list of the chiefs of Succoth and the responsible men, seventy-seven men.
15 Sa’an nan Gideyon ya zo ya ce wa mutanen Sukkot, “To, ga Zeba da Zalmunna, waɗanda kuka yi mini ba’a kuna cewa, ‘Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Me zai sa mu ba mutanenka da suka gaji burodi?’”
So he came to the men of Succoth and said, Here are Zebah and Zalmunna, on account of whom you made sport of me, saying, Are the hands of Zebah and Zalmunna even now in your hand, that we are to give bread to your army who are overcome with weariness?
16 Ya kwashe dattawan garin ya koya wa mutanen Sukkot hankali ta wurin hukunta su da ƙayayyuwan hamada.
Then he took the responsible men of the town and had them crushed on a bed of thorns and sharp stems.
17 Ya rushe hasumiyar Fenuwel ya kuma karkashe mutanen garin.
And he had the tower of Penuel broken down and the men of the town put to death.
18 Sa’an nan ya ce wa Zeba da Zalmunna, “Waɗanne irin mutane ne kuka karkashe a Tabor.” Suka ce, “Mutane kamar ka ne kowane kamar ɗan sarki.”
Then he said to Zebah and Zalmunna, Where are the men whom you put to death at Tabor? And they gave answer, As you are, so were they; every one of them was like a king's son.
19 Gideyon ya ce, “Waɗannan’yan’uwana ne,’ya’yan mahaifiyata. Muddin Ubangiji yana a raye, da a ce kun bar su da rai, da ba zan kashe ku ba.”
And he said, They were my brothers, my mother's sons: by the life of the Lord, if you had kept them safe, I would not put you to death.
20 Da ya juya wajen Yeter, ɗan farinsa, sai ya ce, “Ka kashe su!” Amma Yeter bai zāre takobinsa ba, domin shi yaro ne kawai kuma yana tsoro.
Then he said to Jether, his oldest son, Up! Put them to death. But the boy did not take out his sword, fearing because he was still a boy.
21 Zeba da Zalmunna suka ce masa, “Zo, ka yi da kanka. ‘Yadda mutum yake haka ƙarfinsa.’” Ta haka Gideyon ya matso gaba ya kashe su, ya ɗauki kayan ado daga wuyar raƙumansu.
Then Zebah and Zalmunna said, Up! Put an end to us yourself: for you have a man's strength. Then Gideon got up and put Zebah and Zalmunna to death and took the ornaments which were on their camels' necks.
22 Isra’ilawa suka ce wa Gideyon, “Ka yi mulkinmu, kai, ɗanka da jikanka, domin ka cece mu daga hannun Midiyawa.”
Then the men of Israel said to Gideon, Be our ruler, you and your son and your son's son after him; for you have been our saviour from the hands of Midian.
23 Amma Gideyon ya ce musu, “Ni, ko ɗana, ba za mu yi mulkinku ba. Ubangiji ne zai yi mulkinku.”
But Gideon said to them, I will not be a ruler over you, and my son will not be a ruler over you: it is the Lord who will be ruler over you.
24 Kuma ya ce, “Ina da roƙo guda ɗaya, cewa kowannenku ya ba ni’yan kunne daga rabon ganima.” (Al’adar mutanen Ishmayel ce su sa’yan kunnen zinariya.)
Then Gideon said to them, I have a request to make to you; let every man give me the ear-rings he has taken. (For they had gold ear-rings, because they were Ishmaelites.)
25 Suka ce, “Za mu yi farin cikin ba ka su.” Saboda haka suka shimfiɗa mayafi, kowanne ya sa ɗan kunne ɗaya daga ganimar.
And they gave answer, We will gladly give them. So they put down a robe, every man dropping into it the ear-rings he had taken.
26 Nauyin’yan kunnen zinariyar ya kai shekel ɗari goma sha bakwai, ban da kayan ado, abin wuya da tufafin shunayya waɗanda sarakuna Midiyawa suke sawa ko sarƙoƙin da suke wuyar raƙumansu.
The weight of the gold ear-rings which he got from them was one thousand, seven hundred shekels of gold; in addition to the moon-ornaments and jewels and the purple robes which were on the kings of Midian, and the chains on their camels' necks.
27 Gideyon ya efod da zinariyar, wanda ya ajiye a Ofra, garinsa. Dukan Isra’ila suka shiga yin karuwanci ta wurin yin sujada a can, ya kuwa zama wa Gideyon da dukan iyalinsa tarko.
And Gideon made an ephod from them and put it up in his town Ophrah; and all Israel went after it there and were false to the Lord; and it became a cause of sin to Gideon and his house.
28 Da haka Isra’ilawa suka mallaki Midiyawa ba su kuma sāke tā da kai ba. A zamanin Gideyon ƙasar ta sami zaman lafiya har shekara arba’in.
So Midian was broken before the children of Israel and the Midianites never got back their strength. And the land had peace for forty years, in the days of Gideon.
29 Yerub-Ba’al ɗan Yowash ya koma gida don yă zauna.
And Jerubbaal, the son of Joash, went back to his house and was living there.
30 Yana da’ya’ya saba’in maza da ya haifa, gama yana da mata da yawa.
Gideon had seventy sons, the offspring of his body; for he had a number of wives.
31 Yana kuma da ƙwarƙwara wadda take Shekem, ita ma ta haifa masa ɗa wanda ya ba shi suna Abimelek.
And the servant-wife he had in Shechem had a son by him, to whom he gave the name Abimelech.
32 Gideyon ɗan Yowash ya rasu da kyakkyawan tsufa aka kuma binne shi a kabarin Yowash mahaifinsa a Ofra na mutanen Abiyezer.
And Gideon, the son of Joash, came to his end when he was very old, and his body was put in the resting-place of Joash his father, in Ophrah of the Abiezrites.
33 Ba a daɗe da rasuwar Gideyon ba, sai Isra’ila ta sāke shiga karuwanci suna bauta wa Ba’al. Suka kafa Ba’al-Berit yă zama musu allahnsu ba kuma
And after the death of Gideon, the children of Israel again went after the gods of Canaan and were false to the Lord, and made Baal-berith their god.
34 tuna da Ubangiji Allahnsu, wanda ya cece su daga hannuwan abokan gābansu a kowane gefe ba.
And the children of Israel did not keep in their minds the Lord their God, who had been their saviour from all their haters on every side;
35 Suka kāsa nuna alheri ga gidan Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) saboda abubuwa masu alherin da ya yi musu.
And they were not kind to the house of Jerubbaal, that is, Gideon, in reward for all the good he had done to Israel.

< Mahukunta 8 >