< Mahukunta 8 >
1 To, mutanen Efraim suka ce wa Gideyon, “Me ya sa ka yi mana haka? Me ya sa ba ka kira mu lokacin da ka tafi yaƙi da Midiyawa ba?” Suka zarge shi sosai.
And the men of Ephraim said to him, Why have thou done thus to us, that thou did not call us when thou went to fight with Midian? And they chided with him sharply.
2 Amma ya ce musu, “Me na yi da za a iya kwatanta da abin da kuka yi? Ashe, kalar inabin da Efraim ta yi bai fi dukan girbin inabin da Abiyezer suka yi ba?
And he said to them, What have I now done in comparison with you? Is not the gleaning of the grapes of Ephraim better than the vintage of Abiezer?
3 Allah ya ba da Oreb da Zeyib, shugabannin Midiyawa a hannuwanku. Me na yi da ya fi naku? Da ya faɗi haka sai hankalinsu ya kwanta.”
God has delivered into your hand the rulers of Midian, Oreb and Zeeb, and what was I able to do in comparison with you? Then their anger was abated toward him when he had said that.
4 Gideyon da mutanensa ɗari uku, sun gaji, duk da haka suka yi ta fafarar, suka zo Urdun suka haye shi.
And Gideon came to the Jordan, and passed over, he, and the three hundred men who were with him, faint, yet pursuing.
5 Ya ce wa mutanen Sukkot, “Ku ba wa mutanena burodi; sun gaji, har yanzu ina fafarar Zeba da Zalmunna, sarakunan Midiyawa.”
And he said to the men of Succoth, Give, I pray you, loaves of bread to the people who follow me, for they are faint, and I am pursuing after Zebah and Zalmunna, the kings of Midian.
6 Amma shugabannin Sukkot suka ce, “Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Don me za mu ba wa mayaƙanka burodi?”
And the rulers of Succoth said, Are the hands of Zebah and Zalmunna now in thy hand that we should give bread to thine army?
7 Sai Gideyon ya ce, “Haka ko? To, sa’ad da Ubangiji ya ba da Zeba da Zalmunna a hannuna, zan tsattsaga jikinku da ƙayayyuwan jeji.”
And Gideon said, Therefore when Jehovah has delivered Zebah and Zalmunna into my hand, then I will tear your flesh with the thorns of the wilderness and with briers.
8 Daga nan ya wuce zuwa Fenuwel ya yi irin roƙon nan, amma suka amsa yadda mutanen Sukkot suka yi.
And he went up from there to Penuel, and spoke to them in like manner, and the men of Penuel answered him as the men of Succoth had answered.
9 Saboda haka sai ya ce wa mutanen Fenuwel, “Sa’ad da na dawo da nasara zan rushe wannan hasumiya.”
And he spoke also to the men of Penuel, saying, When I come again in peace, I will break down this tower.
10 To, Zeba da Zalmunna suna a Karkor da mayaƙa wajen dubu goma sha biyar, abin da ya rage ke nan na mayaƙan gabashi; mayaƙa masu takobi dubu ɗari da ashirin ne suka mutu.
Now Zebah and Zalmunna were in Karkor, and their armies with them, about fifteen thousand men, all who were left of all the army of the sons of the east, for there fell a hundred and twenty thousand men who drew a sword.
11 Gideyon ya haura ta hanyar makiyaya, gabas da Noba, da kuma Yogbeha, ya fāɗa wa mayaƙan ta yadda ba su zata ba.
And Gideon went up by the way of those who dwelt in tents on the east of Nobah and Jogbehah, and smote the army, for the army was confident.
12 Zeba da Zalmunna, sarakunan biyu na Midiyawa suka tsere, amma ya bi su ya kama, ya fatattaki dukan mayaƙansu.
And Zebah and Zalmunna fled, and he pursued after them. And he took the two kings of Midian, Zebah and Zalmunna, and discomfited all the army.
13 Sa’an nan Gideyon ɗan Yowash ya komo daga yaƙi ta Hanyar Heres.
And Gideon the son of Joash returned from the battle from the ascent of Heres.
14 Ya kama wani saurayin Sukkot ya tambaye shi, saurayin kuwa ya rubuta masa dukan sunayen shugabanni saba’in da bakwai na Sukkot, da dattawan garin.
And he caught a young man of the men of Succoth, and inquired of him. And he described for him the rulers of Succoth, and the elders of it, seventy-seven men.
15 Sa’an nan Gideyon ya zo ya ce wa mutanen Sukkot, “To, ga Zeba da Zalmunna, waɗanda kuka yi mini ba’a kuna cewa, ‘Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Me zai sa mu ba mutanenka da suka gaji burodi?’”
And he came to the men of Succoth, and said, Behold Zebah and Zalmunna, concerning whom ye taunted me, saying, Are the hands of Zebah and Zalmunna now in thy hand, that we should give bread to thy men who are weary?
16 Ya kwashe dattawan garin ya koya wa mutanen Sukkot hankali ta wurin hukunta su da ƙayayyuwan hamada.
And he took the elders of the city, and thorns of the wilderness and briers, and with them he taught the men of Succoth.
17 Ya rushe hasumiyar Fenuwel ya kuma karkashe mutanen garin.
And he broke down the tower of Penuel, and killed the men of the city.
18 Sa’an nan ya ce wa Zeba da Zalmunna, “Waɗanne irin mutane ne kuka karkashe a Tabor.” Suka ce, “Mutane kamar ka ne kowane kamar ɗan sarki.”
Then he said to Zebah and Zalmunna, What manner of men were they whom ye killed at Tabor? And they answered, As thou are, so were they. Each one resembled the sons of a king.
19 Gideyon ya ce, “Waɗannan’yan’uwana ne,’ya’yan mahaifiyata. Muddin Ubangiji yana a raye, da a ce kun bar su da rai, da ba zan kashe ku ba.”
And he said, They were my brothers, the sons of my mother. As Jehovah lives, if ye had saved them alive, I would not kill you.
20 Da ya juya wajen Yeter, ɗan farinsa, sai ya ce, “Ka kashe su!” Amma Yeter bai zāre takobinsa ba, domin shi yaro ne kawai kuma yana tsoro.
And he said to Jether his firstborn, Up, and kill them. But the youth did not draw his sword, for he feared because he was yet a youth.
21 Zeba da Zalmunna suka ce masa, “Zo, ka yi da kanka. ‘Yadda mutum yake haka ƙarfinsa.’” Ta haka Gideyon ya matso gaba ya kashe su, ya ɗauki kayan ado daga wuyar raƙumansu.
Then Zebah and Zalmunna said, Rise thou, and fall upon us, for as the man is, so is his strength. And Gideon arose, and killed Zebah and Zalmunna, and took the crescents that were on their camels' necks.
22 Isra’ilawa suka ce wa Gideyon, “Ka yi mulkinmu, kai, ɗanka da jikanka, domin ka cece mu daga hannun Midiyawa.”
Then the men of Israel said to Gideon, Rule thou over us, both thou, and thy son, and thy son's son also, for thou have saved us out of the hand of Midian.
23 Amma Gideyon ya ce musu, “Ni, ko ɗana, ba za mu yi mulkinku ba. Ubangiji ne zai yi mulkinku.”
And Gideon said to them, I will not rule over you, neither shall my son rule over you. Jehovah shall rule over you.
24 Kuma ya ce, “Ina da roƙo guda ɗaya, cewa kowannenku ya ba ni’yan kunne daga rabon ganima.” (Al’adar mutanen Ishmayel ce su sa’yan kunnen zinariya.)
And Gideon said to them, I would make a request of you, that ye would give me every man the earrings of his spoil. (For they had golden earrings, because they were Ishmaelites.)
25 Suka ce, “Za mu yi farin cikin ba ka su.” Saboda haka suka shimfiɗa mayafi, kowanne ya sa ɗan kunne ɗaya daga ganimar.
And they answered, We will willingly give them. And they spread a garment, and cast in it every man the earrings of his spoil.
26 Nauyin’yan kunnen zinariyar ya kai shekel ɗari goma sha bakwai, ban da kayan ado, abin wuya da tufafin shunayya waɗanda sarakuna Midiyawa suke sawa ko sarƙoƙin da suke wuyar raƙumansu.
And the weight of the golden earrings that he requested was a thousand and seven hundred shekels of gold, besides the crescents, and the pendants, and the purple raiment that was on the kings of Midian, and besides the chains that were about their camels' necks.
27 Gideyon ya efod da zinariyar, wanda ya ajiye a Ofra, garinsa. Dukan Isra’ila suka shiga yin karuwanci ta wurin yin sujada a can, ya kuwa zama wa Gideyon da dukan iyalinsa tarko.
And Gideon made an ephod of it, and put it in his city, even in Ophrah. And all Israel played the harlot after it there, and it became a snare to Gideon, and to his house.
28 Da haka Isra’ilawa suka mallaki Midiyawa ba su kuma sāke tā da kai ba. A zamanin Gideyon ƙasar ta sami zaman lafiya har shekara arba’in.
So Midian was subdued before the sons of Israel, and they lifted up their heads no more. And the land had rest forty years in the days of Gideon.
29 Yerub-Ba’al ɗan Yowash ya koma gida don yă zauna.
And Jerubbaal the son of Joash went and dwelt in his own house.
30 Yana da’ya’ya saba’in maza da ya haifa, gama yana da mata da yawa.
And Gideon had seventy sons begotten from his body, for he had many wives.
31 Yana kuma da ƙwarƙwara wadda take Shekem, ita ma ta haifa masa ɗa wanda ya ba shi suna Abimelek.
And his concubine who was in Shechem, she also bore him a son, and he called his name Abimelech.
32 Gideyon ɗan Yowash ya rasu da kyakkyawan tsufa aka kuma binne shi a kabarin Yowash mahaifinsa a Ofra na mutanen Abiyezer.
And Gideon the son of Joash died in a good old age, and was buried in the sepulcher of Joash his father, in Ophrah of the Abiezrites.
33 Ba a daɗe da rasuwar Gideyon ba, sai Isra’ila ta sāke shiga karuwanci suna bauta wa Ba’al. Suka kafa Ba’al-Berit yă zama musu allahnsu ba kuma
And it came to pass, as soon as Gideon was dead, that the sons of Israel turned again, and played the harlot after the Baalim, and made Baal-berith their god.
34 tuna da Ubangiji Allahnsu, wanda ya cece su daga hannuwan abokan gābansu a kowane gefe ba.
And the sons of Israel did not remember Jehovah their God, who had delivered them out of the hand of all their enemies on every side,
35 Suka kāsa nuna alheri ga gidan Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) saboda abubuwa masu alherin da ya yi musu.
neither did they show kindness to the house of Jerubbaal, who is Gideon, according to all the goodness which he had shown to Israel.